Aminiya:
2025-04-14@16:20:26 GMT

Tinubu ya tafi Faransa daga nan zai wuce Habasha

Published: 5th, February 2025 GMT

Shugaba Bola Tinubu a wannan Larabar ya bar Nijeriya zuwa ƙasar Faransa domin kai wata ziyara ta ƙashin kai.

Daga nan kuma Shugaba Tinubu zai wuce ƙasar Habasha inda zai halarci taron gamayyar ƙungiyar ƙasashen Afirka ta AU.

NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana Dalilin da farashin citta ya yi tashin gwauron zabo

Mai bai wa Tinubu shawara kan yaɗa labarai, Bayo Onanuga a shafinsa na X, ya ce Tinubu zai tafi Paris ɗin ne gabanin tafiyar da zai yi zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha domin taron ƙungiyar Tarayyar Afirka (AU).

A lokacin taron da za a yi a birnin na Addis Ababa a farkon mako mai zuwa, Shugaba Tinubu zai gana da shugabannin ƙasashen Afirka domin taron ƙungiyar da za a gudanar daga ranar 12 zuwa 16 ga watan Fabrairun 2025.

A yayin ziyararsa a Faransa, Tinubu zai gana da takwaran aikinsa na Faransa Emmanuel Macron.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faransa

এছাড়াও পড়ুন:

Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi

Hanyoyi Biyar Da Mai Kiwon Kajin Gidan Gona Zai Kare Kajinsa Daga Tsananin Zafin Rana.

1- A Tabbatar An Sama Musu Wadacciyar Iska A Dakin Kwanansu:

Ana bukatar mai kiwon kajin ya tabbatar ya sama musu wadatacciyar iska a dakin kwanansu, ana kuma bukatar a yi wa shigifar dakinsu fenti yadda za ta rika rage zafin ranar da kuma samar da kayan koyon da za su sanyaya dakin kwanansu.

Haka kuma, ana bukatar a rika sanya musu na’urar da ke sanyaya daki, wadanda za su rika rage zafin ranar, akalla na’urar ta kasance mai ma’unin yanayi daga 5 zuwa 10°C.

2- Sanya Na’urar Sanya Daki:

Domin samun saukin yanayin zafin rana, ana bukatar mai kiwo ya sanya musu na’ura a dakin kwanansu, domin rika sanyaya dakin, yadda jikinsu zai rika yin sanyi.

Ana kuma bukatar masu kiwon, su rika sanya musu Fanka a dakin kwanansu, wanda hakan zai ba su damar samun wadatacciyar iska.

3- Shayar Da Su Wadataccen Ruwan Sha:

Tanadar musu da wadataccen ruwan sha, na taimaka musu wajen samun sinadaran da za su kara inganta rayuwarsu da kuma jurewa tsananin zafin rana.

Kazalika, ana bukatar masu kiwon su rika zuba musu garin sinadarin ‘glucose da amino acids’, domin kara musu karsashi da kuma kara karfafa garkuwar jikinsu.

4- Sama Musu Da Sauyin Ciyar Da Su Abinci:

Ana bukatar masu kiwonsu, su rika ciyar da su abinci mai dauke da sinadari kamar na ‘Bitamin E da selenium’, wadanda za su taimaka wa lafiyarsu.

Wadannan sinadarai, na matukar bayar da gudunmawa wajen ba su kariya daga jin tsananin zafin rana.

5- Sanya Ido Kan Yiwuwar Barkewar Wata Cuta:

Ana bukatar mai kiwon kajin ya tabbatar yana yawan sanya ido kan kajin, domin gano wasu alamomin da za su iya sanya su ji tsananin zafin rana ko kuma kamuwa da wasu kwayoyin cuta, musamman domin daukar matakan gaggawa na kare lafiyarsu.

Ana kuma bukatar mai kiwonsu ya tabbatar yana ciyar da su abinci mai gina jiki, wanda hakan zai taimaka musu daga saurin kamuwa da kwayoyin cututtuka.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • Inganta Rayuwar Al’umma: Amurka Da Ƙungiyar Kasuwanci Ta Nijeriya Sun Karrama Gwamna Lawal
  • Mutum ɗaya ya mutu a faɗan ƙungiyar asiri a Maiduguri
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro
  • Hanyoyi Biyar Na Kare Kajin Gidan Gona Daga Tsananin Zafi
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing