Aminiya:
2025-03-23@22:41:30 GMT

Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trn

Published: 5th, February 2025 GMT

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya buƙaci a ƙara adadin kasafin kuɗin shekarar 2025 daga Naira tiriliyan 49.7 zuwa Naira tiriliyan 54.2.

Wannan buƙata na ckkin wata wasiƙa da ya aike wa Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, wadda aka karanta a zaman majalisar na ranar Laraba.

Tinubu zai tafi Faransa daga nan ya zarce Habasha NAHCON ta tsawaita wa’adin biyan kuɗin Hajjin bana

A baya, Tinubu ya gabatar wa Majalisar Dokoki kasafin Naira tiriliyan 49.

7 a ranar 18 ga watan Disamba. 2024.

Sai dai a cikin wasiƙarsa, ya bayyana cewa ƙarin da aka yi ya samo asali ne daga ƙarin kuɗaɗen shiga da hukumomin gwamnati suka tara.

Wannna ya haɗa da Naira tiriliyan 1.4 da Hukumar Tara Haraji ta Ƙasa (FIRS) ta samu, da Naira tiriliyan 1.2 da Hukumar Kwastam ta samu, da Naira tiriliya. 1.8 da wasu hukumomin gwamnati suka samu.

Bayan karanta wasiƙar, Shugaban Majalisar Dattawa, ya tura buƙatar ga Kwamitin Kasafin Kuɗi don yin nazari cikin gaggawa.

Haka kuma, ya tabbatar da cewa za a kammala duba kasafin kuɗin tare da amincewa da shi kafin ƙarshen watan Fabrairu.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Samun Kuɗaɗen Shiga Naira tiriliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas

Majalisar Wakilai ta ƙaryata zargin da ake mata na karɓar cin hanci domin amincewa da dokar ta-ɓaci da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya ayyana a Jihar Ribas.

Ɗan majalisa mai wakiltar mazabar Gwaram a Jihar Jigawa, Hon. Yusuf Shittu Galambi, ya kare majalisar yayin da ake ta cece-kuce kan batun.

Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia

Wasu ƙungiyoyi na zargin majalisar da yin ƙasa a gwiwa wajen yanke hukunci kan lamarin.

A wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, Galambi, ya ce babu gaskiya a zargin da ake yi cewa an tursasa ’yan majalisa ko an ba su na goro don su amince da matakin shugaban ƙasa.

Ya bayyana cewa yawancin mambobin majalisar sun goyi bayan matakin ne domin kare dimokuraɗiyya da kuma tsare muradun al’ummar Jihar Ribas.

“Mun yanke shawarar ne bisa kishin ƙasa, haɗin kan siyasa, zaman lafiya, da kare dimokuraɗiyya,” in ji shi.

Ya ce ya yi mamakin yadda wasu kafafen yaɗa labarai ke baza jita-jita cewa an tilasta musu su amince da dokar ta-ɓaci tare da karɓar daloli.

A cewarsa, ya kamata ’yan Najeriya su fahimci cewa ’yan majalisa suna aiki ne don ganin an samar da tawagar sulhu kafin wa’adin dokar ta-ɓacin ta ƙare.

Ya jaddada cewa dole ne a kare dimokuraɗiyya a Najeriya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fiye Da Dalibai 4,200 Suka Amfana Da Tallafin Ilimi Na Sanata Solomon Adeola
  • Dalilan Gwamnatin Tarayya Na Zuba Naira Tiriliyan 1.5 A Bankin Aikin Noma -Kyari
  • Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99
  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • Gwamnati ta kama mutum 347 kan haƙar ma’adanai ba bisa ƙa’ida ba
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Kotu Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha
  • Kotun Ta Dakatar Da INEC Karɓar Buƙatar Yin Kiranye Ga Senata Natasha
  • Majalisar Dokokin Nijeriya Ta Zama Ƴar Amshin Shata — Kwankwaso