Saura ƙiris Bello Turji ya zo hannu – Ministan Tsaro
Published: 5th, February 2025 GMT
Ministan Tsaro, Muhammad Badaru Abubakar, ya bayyana cewa sun kusa da kama ƙasurgumin ɗan ta’addan nan da ya addabi yankin Arewa Maso Yamma, Bello Turji.
Ministan ya ƙara da cewa Gwamnatin Tarayya tana da tabbacin cewa matsalar tsaro za ta zama tarihi kafin ƙarshen shekarar 2025.
Sarkin Jiwa a Abuja ya yi rashin mahaifiya Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trn
“Shugaban ƙasa na cewa yaushe matsalar tsaro za ta ƙare, saboda lokacin da ya kamata ta ƙare ya yi.
“A wani zama da muka yi da shi da shugabannin hafsoshin tsaron, an tattauna sosai, kuma shugaban ya ce su faɗa masa yaushe matsalar za ta ƙare, suka ce da yardar Allah zuwa ƙarshen shekarar nan,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa: “Sun ce ko matsalar ba ta ƙare gaba ɗaya ba, to za a ga sauƙin da kowa zai gani ya kuma ji daɗi.”
A wani taron da aka yi tare da shugabannin tsaro, Badaru, ya ce Shugaban Ƙasa ya bayyana cewa yana tsammanin matsalar tsaro za ta ƙare kafin ƙarshen shekara mai zuwa.
Hakazalika, ya ce idan matsalar ba ta ƙare, gwamnatin za ta ɓullo da sabbin dabaru domin murƙushe ta’addanci a yankin da ma Najeriya baki ɗaya.
A yayin tattaunawa da BBC Hausa, Ministan ya bayyana cewa duk da a yanzu ba a kama Turji ba, amma suna da labarin ya fara guje-guje, kuma nan ba da jimawa ba zai shiga hannu.
Ministan ya tabbatar da cewa tsare-tsaren da Gwamnatin Tarayya da hafsoshin tsaro suke aiwatarwa, za su kai ga gagarumar nasara wajen inganta tsaro a Najeriya.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Arewa maso yamma Ministan tsaro Muhammad Badaru Abubakar
এছাড়াও পড়ুন:
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’ila Bagaei ya godeawa ministan harkokin wajen kasar Omman kan yadda ya shirya ya kuma gabatar da tattaunawa tsakanin JMI da Amurka a birnin Mascat da kuma kai kawon da yayi a tsakanin bangarorin biyu.
Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Bagaei yana bayyana haka a wani sakon da ya aika a cikin shafinsa na X a jiya Asabar, ya kuma aika da sakon ne a dai dai lokacinda ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi yana kan hanyarsa ta dawowa Tehran, bayan tattaunawar. Ya kuma kara da cewa yana fatan Badr bin Hamad Al Busaidi zai ci gaba da wannan kokarin a ranar Asabar mai zuwa inda bangarorin biyu zasu sake haduwa, sannan har zuwa karshen tattaunawar. Bayan kammala tattaunawar dai, shugaban tawagar JKI a tattaunawar kuma ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana a shafinsa na X kan cewa, tattaunawar ta yi armashi.