Da yake magana ta wayar tarho game da mummunar gobarar, Shugaban ƙaramar hukumar Kaura-Namoda, Comrade Mannir Muazu Haidara, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce yana kan hanyarsa domin duba halin da ake ciki kuma zai bayar da karin bayani daga baya.

.

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Gobara Makarantar Allo Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Borno, ta daƙile wani yunƙuri da ’yan bindiga suka yi na sace wani mutum a Sabon Garin Lassa da ke Ƙaramar Hukumar Askira Uba.

Rundunar ta kuma cafke wasu mutum uku tare da ƙwato wata bindiga ƙirar gida a hannunsu.

Babban mai kai wa Bello Turji makamai ya shiga hannu NAJERIYA A YAU: Dalilan Da Ba Za Mu Sauke Farashin Burodi Ba —’Yan kasuwa

Majiyoyin tsaro sun shaida wa Zagazola Makama cewa, lamarin ya faru ne a ranar 20 ga watan Fabrairu da misalin karfe 1 na dare.

Wasu ’yan bindiga huɗu suka kai hari gidan Mohammed Abubakar, mazaunin Sabon Gari Lassa, da nufin sace shi.

“Wanda suka yi niyyar sacewa ya yi ƙoƙarin kare kansa da adda, lamarin da ya tilasta wa maharan tserewa ba tare da sun cimma burinsu ba”, in ji majiyar.

Bayan haka, Abubakar, ya gaggauta kiran ’yan sanda, inda tare da haɗin gwiwar ’yan banga, jami’an tsaro suka bi sahun ’yan bindigar zuwa maɓoyarsu.

A sakamakon haka, rundunar ‘yan sanda ta cafke mutum uku da ake zargi, dukkaninsu mazauna ƙauyen Gajali da ke Ƙaramar Hukumar Askira Uba.

“Haka kuma an ƙwato wata bindiga da aka ƙera a gida daga hannun waɗanda ake zargin,” in ji majiyar.

Rundunar ’yan sandan jihar, ta yaba da yadda jami’an tsaro suka mayar da martani cikin gaggawa, tare da yin kira ga al’umma da su kasance masu lura da duk wani abu da ba su saba gani ba.

Ta kuma buƙaci su gaggauta kai rahoto ga jami’an tsaro domin ɗaukar mataki a kan lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DRC : Kwamitin Tsaro Na MDD, Ya Yi Da Goyan Bayan Da Rwanda Ke Bai Wa ‘Yan Tawayen M23
  • ’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno
  • ‘Yansanda Sun Kwato Motoci 7 Da Aka Sace Da Taimakon Na’urar e-CMR A Kano
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 12, sun sace wasu a Zariya
  • Gobara ta ƙone gidaje, dabobbi da kayan abinci a Kano
  • An Rantsar Da Sabbin Shugabannin Kungiyar Manyan Sakatarorin Jihar Zamfara
  • ’Yan bindiga sun Kashe mutum 2, sun sace manoma 10 a Neja
  • Rigima ta sake kaurewa tsakanin PDP da APC a Zamfara
  • Mutum 11 sun kuɓuta daga hannun Boko Haram a Borno
  • Mutane Da Dama Sun Jikkata Sakamakon Fashewar Wani Abu A Kasuwar Zamfara