Aminiya:
2025-04-16@08:18:58 GMT

’Yan sanda sun kama baƙin haure 165 a Kebbi

Published: 5th, February 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi, ta kama wasu mutum 165 da suka shigo Najeriya ba tare da izini ba.

Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, Nafi’u Abubakar, ya ce an kama mutanen ne a Birnin Kebbi.

Gobara ta yi ajalin almajirai 17 a Zamfara Tinubu ya ƙara kasafin kuɗin 2025 zuwa N54.2trn

Ya ce 35 daga cikinsu ’yan asalin ƙasar Burkina Faso ne, yayin da 11 ’yan asalin Jamhuriyar Benin ne.

Akwai kuma mutum biyar daga Nijar, huɗu daga Mali, sai mutum 110 ’yan ƙasar Ivory Coast.

Ya ce mutanen ba su da takardun izinin shigowa Najeriya kuma an same su da aikata damfara.

Rundunar ta bayyana cewa an miƙa su ga Hukumar Shige da Fice ta Ƙasa da ke Jihar Kebbi, domin gudanar da bincike da kuma ɗaukar matakin da ya dace.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Najeriya Rashin Izini

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kebbi Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai A Saudiyya

Gwamnatin Jihar Kebbi ta kammala shirye-shiryen daukar nauyin dalibai 70 zuwa Masarautar Saudiyya domin karatun digiri a fannoni na addini da na zamani.

Wannan na daga cikin shirin Kaura Capacity Building Project 2025 karkashin ma’aikatar kula da harkokin addinai ta jihar.

A yayin wani taron manema labarai, mai bai wa Gwamna shawara kan harkokin addinali, Injiniya Imran bn Usman, ya bayyana cewa kowanne daga cikin kananan hukumomi 20 na jihar za su ba da sunayen dalibai uku, yayin da aka ware wa babban birnin jihar, Birnin Kebbi, guraben dalibai 10.

Ya bayyana cewa, gwamnatin jihar ce za ta dauki nauyin tafiyar daliban zuwa Saudiyya, yayin da gwamnatin Saudiyya za ta dauki nauyin karatunsu da walwalarsu bayan isarsu.

Mai ba da shawarar ya kara da cewa, ana sa ran kowacce karamar hukuma za ta gabatar da dalibai maza biyu da mace daya, don neman guraben karatun digiri a fannin addinin Musulunci ko sauran fannoni na zamani.

Ya kuma kara da cewa, an kammala shirin tura limaman masallatai Jumu’a zuwa kasashen waje domin horo na gajeren lokaci a fannin yadda ake gabatar da huduba da Hadisi, don kara inganta tasirinsu yayin gabatarda Sallah.

 

Daga Abdullahi Tukur

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Kashe Mutane Da Dama A Tsakiyar Najeriya
  • Gwamnatin Kebbi Za Ta Dauki Nauyin Karatun Dalibai A Saudiyya
  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • ‘Yansanda Sun Gano Haramtaccen Wurin Hada Makamai A Kano
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo