Jami’in tsaron kasar Iran ya karyata sabuwar da’awar jaridar New York Times ta kasar Amurka

Jami’in tsaron kasar Iran ya musanta wasu sabbin zarge-zargen da jaridar New York Times ta Amurka ta wallafa game da zargin Iran cewa tana bunkasa ayyukannta na kera makaman kare dangi.

Jami’in tsaron ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Tasnim cewa: Ikirarin da jaridar New York Times ta yi game da wata kungiyar asiri ta masana kimiyyar Iran da ke aikin samar da hanyoyin kera makaman nukiliya cikin sauri, ba komai ba ne illa shirme da zage-zage marasa tushe da kan gado.

Jami’in ya kara da cewa: “Wadannan rudun tunani ba su da alaka da gaskiya, kuma kawai labaran karya ne da wasu kafafen yada labarai na Amurka ke yi don goyon bayan ajandar fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ‘yar mamaya Benjamin Netanyahu.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta

Wata ’yar kasar Jamus mai suna Alexandra Hildebrandt mai shekara 66 ta ja hankalin jama’a bayan ta haifi ɗanta na 10 ba tare da maganin haihuwa ba.

Haihuwar ta faru ne a ranar 19 ga Maris a Asibitin Charité da ke Berlin da taimakon likita.

Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato

Ta bayyana hakan ne yayin wata tattaunawa da ta yi da Jaridar TODAY.com a ranar Laraba, 26 ga watan Maris.

A cewar Hildebrandt, ta rawa wa jaririn suna Philipp, wanda ya zo da nauyin kilo 7, kuma yana cikin koshin lafiya.

Ta bayyana shi a matsayin wanda ya dace da ’ya’yanta da ke da yawa, wanda ya haɗa da yara masu shekaru tsakanin 2 zuwa 46.

“Babban iyali ba kawai wani abu ne mai ban mamaki ba, amma duk da haka, yana da mahimmanci don renon yara yadda ya kamata,” in ji ta a cikin imel.

Hildebrandt, wanda ke kula da gidan tarihi na Wall Museum a Checkpoint Charlie a Berlin, ba bakon abu ba ne wajen jan hankalin jama’a.

Rayuwarta cike take da tarihi, domin zama uwa a wurinta abin mamaki ne.

Duk da shekarunta, ta nace cewa ciki ba a tsara shi ta hanyar kimiyya, amma ya faru ne ta dabi’a.

Mahaifiyar ta bayyana cewa, tana rayuwa cikin matukar aiki.

Kafin haihuwar Philipp, ta bayyana wa Jaridar Jamus ta Bild cewa, “Ina cin abinci cikin koshin lafiya, ina iya yin ninkaya tsawon awa guda a matsayin motsa jiki kuma ina tafiyar tsawon awa biyu.”

Likitanta, Dokta Wolfgang Henrich ya tabbatar da cewa, cikin nata ya daidaita, yana mai bayyana shi a matsayin cikin da ba shi da matsala sosai,” kodayake Hildebrandt ta yi haihuwa takwas a baya duk ta hanyar tiyata.

‘Ya’ayanta 10 sun hada da tagwaye, Elisabeth da Madimilian, dukansu shekarunsu 12, wadanda suke nuna cewa, rayuwar Hildebrandt a matsayin uwa cike take da matakai iri-iri.

Amma haihuwar ’ya’ya a irin waɗannan shekarun na tsufa ba kowa ba ne ke samun hakan.

Henrich ya yi gargaɗin cewa, masu juna biyu a shekarun tsufa na rayuwa cikin haɗari.

Ya bayyana cewa, “matsaloli irin su hawan jini da haihuwar jariri kafin mako 37 da kuma al’amurran da suka shafi zuciya da jijiyoyin jini yawanci na karuwa da shekaru”.

Ta ce, tana ta samun sakonnin taya murna da soyayya daga abokanta da danginta bayan sanar da haihuwar Philipp.

“Na yi ta samun sakonnin fatan alheri,” in ji ta TODAY.com.

A halin da ake ciki, masana kiwon lafiya sun yi imanin cewa, ba koyaushe shekaru suke taƙaita batun haihuwa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Ta Bukaci Amurka Da Ta Yi Watsi Da Matsawa Sauran Kasashe Lamba
  • Aljeriya ta yi barazanar korar jami’an diflomasiyyar Faransa 12
  • ’Yar shekara 66 ta haifi ɗanta na 10 da kanta
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • Iran Ta Ce Za’a Gudanar Da Zagaye Na Gaba Tsakaninta Da Amurka Ne A Birnin Roma Na Kasar Italiya
  • Kasashen Larabawa Na Yankin Tekun Farisa Sun Yi Fatan Al-Khairi Ga Iran Da Amurka A Tattaunawar Shirin Nukliyar Kasar
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Sharhi: Tattaunawa Zagaye Na Farko Tsakanin Iran Da Amurka A Oman