Jami’in tsaron kasar Iran ya karyata sabuwar da’awar jaridar New York Times ta kasar Amurka

Jami’in tsaron kasar Iran ya musanta wasu sabbin zarge-zargen da jaridar New York Times ta Amurka ta wallafa game da zargin Iran cewa tana bunkasa ayyukannta na kera makaman kare dangi.

Jami’in tsaron ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na Tasnim cewa: Ikirarin da jaridar New York Times ta yi game da wata kungiyar asiri ta masana kimiyyar Iran da ke aikin samar da hanyoyin kera makaman nukiliya cikin sauri, ba komai ba ne illa shirme da zage-zage marasa tushe da kan gado.

Jami’in ya kara da cewa: “Wadannan rudun tunani ba su da alaka da gaskiya, kuma kawai labaran karya ne da wasu kafafen yada labarai na Amurka ke yi don goyon bayan ajandar fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ‘yar mamaya Benjamin Netanyahu.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

 Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!

A wata hira da tashar talabijin din, manzon musamman na Amurka a yankin gabas ta tsakiya Steve Witkoff ya rubuta a shafinsa na; X cewa; Sakon da Trump ya aike wa  Tehran ba ta nufin yin barazana.

Manzon na Amurka ya riya cewa;wasikar ta kunshi cewa; Ni shugaban kasa ne mai son zaman lafiya , abinda  nake son bayyanawa kenan, don haka babu bukatar a yi magar yaki. Wajibi ne mu zauna mu tattauna.”

Wittkoff ya kuma ce; Da akwai hanyoyi na bayan fage da ake tatatunawa da Iran.

Har ila yau ya kara da cewa; Abinda Trump yake so shi ne warware sabanin da ake da shi.

Shafin watsa labaru na Axos ya bayyana cewa; Waskiyar da Trump din ya aiko wa Iran ta kunshi ayyana wa’adin watanni biyu na cimma  sabuwar yarjejeniya Nukiliya.

Wannan sabon matsayin na Amurka dai ya zo ne,bayan da mahukunta a jamhuriyar musulunci ta Iran suka bayyana cewa; Amurkan ba za ta sami wani abu daga Iran ba ta hanyar barazana.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
  • Iran Ce Kasar Wacce Ta Fi Shigar Da Kayakin Kasuwanci Zuwa Kasar Afganistan A Shekarar Da Ta Gabata
  •  Amurka: Turmp Yana Son Yin Yarjejeniya Ne Da Iran Ba Yaki Ba!
  • Iran da UAE sun kirayi Isra’ila da Amurka da su kawo karshen hare-harensu a Gaza da Yemen
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  •  HKI: Ana Samun Koma Bayan Sojojin Sa-Kai Da Suke
  • Jagora: Amurka Ta Kwana Da Sanin Cewa Ba  Wata Riba Da Za Ta Ci Ta Hanyar Yi Wa  Iran Barazana
  • Shugaban Kasar Iran Ya Bukaci Hadin Kai Tsakanin Iraniyawa Saboda Amfanin Kasar
  • Iran, ta yi Tir da kwamatin tsaro kan rashin tabaka komai na takawa Amurka da Isra’ila birki
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka