Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Ce Matsin Lamba Kan Iran Ba Zai Yi Tasiri Ba
Published: 5th, February 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Tsananta matsin lamba da ake son dauka kan Iran ba zai yi wani tasiri ba
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Manufar matsin lamba da shugaban Amurka Donald Trump ya dauka kan Iran za ta sake yin kasa a gwiwa tare da rashin nasara.
Araqchi ya bayyana a cikin wata sanarwa da ya fitar bayan kammala zaman majalisar ministocin a yau Laraba, inda ya ce mafi girman matsin lamba shi ne gwajin da aka yi kan kasar Iran da bai yi nasara ba, ya kara da cewa; Idan babban batu shi ne cewa Iran ba ta kama hanyar mallakar makamin nukiliya ba, to hakan na iya yiwuwa kuma babu wata matsala a wannan bangaren.
Araqchi ya jaddada cewa: Matsayin Iran a bayyane yake, kuma ita mamba ce ta NPT (yarjejeniyar hana yaduwar makaman nukiliya) kuma fatawar Jagoran juyin juya halin Musulunci tana da inganci da kuma bayyana irin nauyin da ke wuyan kasar ta Iran.
Shugaban Amurka Donald Trump ya fada a yammacin jiya Talata bayan sanya hannu kan wata doka mai dawo da manufar matsin lambar siyasa kan kasar Iran cewa: Za su kakaba wa Iran “takunkumi mai tsanani” tare da dakatar da fitar da man da take fitarwa.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha A cikin Kasar
Labaran da suke fitowa daga kasar Ukraine sun bayyana cewa, gwamnatin kasar tana son karban iko da bututun iskar gas na kasar Rasha wanda yake yammacin kasar da Turai, wanda kuma yake kai iskar gasa zuwa kasashen Turai.
An gina bututun tun zamanin tarayyar Soviet kuma kasashen biyu suna samun kudade masu yawa daga wannan bututun.
Gwamnatin kasar Amurka dai tana son ta dawo da kudaden da ta kashewa kasar Ukraine na makamai wacce ta karba a likacin shugaban Biden. Daga cikin dai Amurka ta bukaci Ukraine ta bada ma’adinanta na kimani dalar Amurka biliyon $500.
Wasu rahotanni sun bayyana cewa jami’an gwanatocin kasashen Amurka da Ukraine sun tattauna wannan batun a ranar jumma’an da ta gabata, don tattauna batun irin ma’adinan da kasar Ukraine zasu bawa Amurka saboda biyan kudaden da take binta basgi. Har’ila yau Amurkawan sun gabatar da shawarar kasashen biyu su hada giwa don samun riba tare a aikin hakar Ma’adinan.