Sabbin Matakan Harajin Amurka: Da Alama Kaikaiyi Zai Koma Kan Mashekiya
Published: 5th, February 2025 GMT
“Canada, Mexico da Sin su ne suke sayen rabin duk kayayyakin amfanin gona da Amurka ke fitarwa. Kasuwanni ne da muke bukata babu makawa don raya tattalin arzikin Amurka. Sanya haraji kan manyan kasuwannin fitar da kayayyakin guda uku na noma da kiwo na Amurka, musamman na dogon lokaci zai haifar da mummunan sakamako,” in ji sanarwar.
Tabbas! abin da manoman suka fada gaskiya ne, domin ko a shekarar 2018, karin harajin da Amurka ta kakkaba a kan kayayyakin kasar Sin, ya janyo kasar ta Sin wadda a baya ita ce ta fi shigo da wake na Amurka, ta sanya karin harajin kashi 25 cikin 100 na ramuwar gayya kan kayayyakin da Amurka ke fitarwa. Kuma a yanzu ma, Sin ta lashi takobin mayar da martani inda tuni, a farkon makon nan ta fitar da sanarwa daga ma’aikatar cinikayya da ma’aikatar kudi a kan fara aiwatar da martaninta ga Amurka.
Daga ciki, kasar Sin ta sanya harajin kashi 10% zuwa 15% kan wasu kayayyakin da ake shigowa da su daga Amurka, wanda zai fara aiki daga ranar 10 ga Fabrairun nan. Sannan, Sin ta yanke shawarar shigar da rukunin kamfanonin US PVH da Illumina a cikin jerin kamfanonin da ba su da tabbas. Kana ta shigar da kara a gaban Kungiyar Kasuwanci ta Duniya, watau WTO. Bugu da kari, Sin ta hana fitar da wasu sinadarai masu muhimmanci da ake amfani da su wajen hada kayayyakin lantarki da na karafa.
Fitina dai a kwance take, kuma la’ana tana kan duk wanda ya tayar da ita! (Daga Abdulrazaq Yahuza Jere)
এছাড়াও পড়ুন:
Za’a Gudanar Taron Tattaunawa Tsakanin Rasha Ta Amurka A Karo Na Biyu 2 A Birnin Rayad na Kasar Saudiya
A gobe Litinin 24 ga watan Maris ne tawagogin masu tattaunawa na kasashen Amurka da Rasha zasu hadu a birnin Rayida na kasar Saudiya don ci gaba da tattaunawan da suka fara a yan makonnin da suka gabata dangane da yakin da ke faruwa a Ukraine, shekaru fiye da 3 da suka gabata, da kuma dangantaka a tsakanin kasashen biyu.
Kamfanin dillancin labaran Sputnik na kasar Rasha ya nakalto Yury Ushakov mai bawa shugaba Putin shawara kan al-amurin siyasa yana fadar haka. Ya kuma kara da cewa Sanata Georgy Karasin ne zai jagoranci tawagar masu tattaunawa ta kasar Rasha sannan ta kasar Amurka an rika an samar da tawagar, wasu zata hadu da na Rasga a gobe litin a birnin Riyad.
Kafin haka dai shugaban kasar Rasha Vladimir Putin sun tattauna da tokwaransa na kasar Amurka Donal Trump kan al-amura da dama wadanda suka shafi yakin a Ukraine da tsagaita budewa juna wuta na wata guda da kuma wasu al-amura.
Karsin daga karshe ya ce yana fatan tattaunawan zata yi armashi.