Kamfanin hakar ma’adinai na Jiuling Lithium, na kasar Sin, na shirin zuba jarin sama da dala miliyan 200 a domin haƙar lithium a Endo da ke jihar Nasarawa.

A ziyarar da gwamna Abdullahi Sule ya kai, shugaban kamfanin, Mista Xiong Jin, ya jaddada aniyarsu ta gina daya daga cikin manyan masana’antar samar da lithium a jihar.

Ya kuma bayyana cewa ma’aikatan da aka dauka aiki a wurin za su sami mafi karancin albashi na N500,000.

Saurayi Ya Fille Kan Budurwarsa A Nasarawa Gwamna Sule Ya Rushe Majalisar Zartarwar Nasarawa, Ya Sauke Sakataren Gwamnati

Gwamna Sule ya bukaci matasa da su rungumi sana’o’in hannu domin cin gajiyar guraben ayyukan yi a fannin hakar ma’adinai.

Ya kuma tabbatar da cewa gwamnatin jihar tare da hadin gwiwar hukumomin tarayya na daukar matakan da suka dace domin ganin an samu nasarar aikin.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dangote Ya Koma Matsayi Na 86 A Jadawalin Masu Arziƙin Duniya

Arziƙin hamshakin attajirin nan ɗan jahar Kano Alhaji Aliko Dangote ya ninka na bara inda ya ƙaru zuwa dala biliyan 23.9, wanda hakan yasa ya cigaba da kasancewa mutumin da yafi kowa dukiya a nahiyar Afrika kuma ya koma matsayi na 86 a jadawalin masu kudin Duniya kamar yadda mujallar Forbes mai ƙididdiga akan masu kuɗin Duniya ta fitar, Forbes ta zaɓi Aliko Dangote a matsayin mutum na 144 mafi arziƙi a duniya a shekarar 2024 da dala biliyan 13.4.

Forbes ta yi kiyasin cewa dukiyar Dangote ta kai dala biliyan 23.9, musamman saboda hannun jarin sa na kashi 92.3 na matatar man dangote, Aliko Dangote mai shekaru 67, ya sake zama ɗaya daga cikin manyan attajirai 100 a duniya, matsayin da bai riƙe ba tun shekarar 2018, a cewar Forbes Real-Time Billionaires List.

Zargin Damfara: Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Ma’aikacin Dangote Kamfanin Harhaɗa Mota Na Dangote  Ya Kera Peugeot 3008 GT A Kaduna

Wannan ya sa ya zarce ɗan Afrika ta Kudu Johann Rupert, wanda ke matsayi na 161 a duniya yana da dukiyar da aka ƙiyasta ta kai dala biliyan 14.4, kuma ya zarce Mike Adenuga, wanda shi ne na biyu mafi arziƙi a Nijeriya kuma yake na 481 a duniya, inda yake da dukiyar da ta kai dala biliyan 6.8.

Dangote ya shiga harkar mai a shekarar da ta gabata ta hanyar gina matatar mai mafi girma a Afirka, bayan shekaru 11, ya zuba jarin dalar Amurka biliyan 23, matatar Dangote ta fara aiki a bara inda matatar da ke kan wani yanki mai girman eka 6,200 a yankin Free Zone na Lekki, za ta sarrafa ganga 650,000 a kowace rana (b/d), wanda zai zama matatar mai ta bakwai mafi girma a duniya kuma mafi girma a Afrika.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda Za A Kare Yara Daga Barazanar Intanet
  • Jihar Kano Ta Samar Da Wani Salo Na Bunkasa Ilmin Addinin Musulunci A Jihar
  • Gwamna Namadi Ya Kaddamar Da Shirin Da’awah Na Mata A Jihar Jigawa
  • Dangote Ya Koma Matsayi Na 86 A Jadawalin Masu Arziƙin Duniya
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Matasan Jihar Jigawa Sun Karrama Gwamna Umar Namadi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bai Wa Jihar Jigawa Kayayyakin Noma Na Sama Da Naira Biliyan 5
  • Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro ta Kano
  • Abba ya sanya hannu kan dokar kafa rundunar tsaro a Kano