Kwamishinan ‘Yansandan Kano Ya Gana Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Inshorar Motoci
Published: 6th, February 2025 GMT
Kwamishinan ‘yan sandan jihar Kano, CP Salman Dogo Garba, ya gana da masu ruwa da tsaki a harkokin sufuri domin tattauna yadda ake ci gaba da aiwatar da aikin inshorar motoci na wasu motocin da ke bin hanyoyin jihar Kano.
Taron wanda ya samu halartar shuwagabannin kungiyar ma’aikatan sufuri ta kasa (NURTW), kungiyar masu safara a tituna ta Najeriya (NARTO), kungiyar ma’aikatan sufurin mota ta kasa (RTEAN), da kuma shugaban tashar motocin Kano Line da nufin tabbatar da bin ka’idojin inshora.
CP Dogo ya yabawa masu ruwa da tsaki bisa hadin kan da suka bayar, inda ya ce sama da kashi 85% na masu ababen hawa sun mallaki takardar inshorar motocin da ake bukata daga ranar farko da aka fara aiwatar da su.
Ya kuma ja hankalin jama’a da su ci gaba da bin ka’idojin zirga-zirgar ababen hawa, inda ya jaddada muhimmancin kiyaye hanya.
Rundunar ‘yan sandan jihar Kano za ta ci gaba da aiwatar da ka’idojin inshorar motoci na wasu kamfanoni, bisa ga umarnin babban sufeton ‘yan sanda, IGP Kayode Adeolu Egbetokun. CP Dogo ya bukaci masu ruwa da tsaki da su wayar da kan ‘yan kungiyar su hada kai da ‘yan sanda tare da kai rahoton duk wani abu da ake zargi.
Jama’a na iya kai rahoto ga ofishin ‘yan sanda mafi kusa ko ta hanyar tuntuɓar masu zuwa: 08032419754, 08123821575, ko 09019292926.
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Inshara
এছাড়াও পড়ুন:
UNICEF: Yara a Gaza suna fama da matsalar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba
Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya sanar da cewa, yara a Gaza suna fuskantar matsakar kwakwalwa da ba a taba ganin irinsa ba a kan kananan yara.
“Ba mu da wani bayani a tarihin wannan zamani dangane da ke bukatar tallafin lafiyar kwakwalwa kamar yaran Gaza,” in ji mai magana da yawun UNICEF James Elder a wani taron Majalisar Dinkin Duniya a Geneva.
Sannan kuma jami’in ya yi Allah wadai da tauye hakkin yara da ake yi da gangan a Gaza, ya kuma bukaci masu karfin fada a ji a duniya da su dauki mataki.
Ya kara da cewa an toshe alluran rigakafi 180,000 na rigakafin yara masu mahimmanci, da na’urorin saka jariran da ba su kai ga lokacin haihuwa ba, inda Isra’ila ta hana shigar da wadannan kayayyakia cikin yankunan zirin gaza.
Babban jami’in na UNICEF ya ce, daukar irin wadannan matakana kan yara yana a matsayin babban laifi wanda ka iya zama laifin yaki bisa dokoki na kasa d akasa.
A kan haka ya kara jaddada kiransa ga kasashe masu karfin fada a ji da su sauke nauyin da ya rataya a kansu kan batun Gaza.