Gwamnatin Niger Ta Karbi Yara 21 Da Aka Ceto
Published: 6th, February 2025 GMT
Gwamnatin jihar Neja ta karbi yara ashirin da daya da aka kama a kan iyakar Najeriya da jamhuriyar Nijar yayin da ake safarar su zuwa Sudan.
Mataimakin gwamnan jihar, Kwamared Yakubu Garba wanda ya bayyana haka a lokacin da yake karbar yaran a madadin gwamnatin jihar Neja a Minna, ya ce an kama yaran ne a cikin kasashen Kamaru da Mali da Jamhuriyar Nijar da kuma Sudan.
Kwamared Yakubu Garba ya bayyana cewa yaran da aka ceto ‘yan karamar hukumar Magama ne a jihar Neja, amma ya yaba da kokarin gwamnatin tarayya da hukumomin tsaro da kuma hukumar fataucin bil’adama bisa nasarar ceto yaran.
Ya ci gaba da cewa ta’addancin ya saba wa kundin tsarin mulkin Najeriya sashe na 34 karamin sashe na 1 da sashe na 13 na kundin tsarin mulkin kasa da ya haramta duk wani nau’in safarar mutane a kasar.
Da yake mayar da martani, daya daga cikin iyayen yaran da aka ceto, Jamilu Usman wanda ya bayyana ‘ya’yansa biyu Umar Jamilu mai shekaru 6 da Maruf Jamilu mai shekaru 5 ya bayyana cewa Malam Abubakar sananne ne a wurinsu wanda ya yi karatu a Jamhuriyar Nijar.
Ya bayyana cewa sun ba wa ‘ya’yansu damar tafiya da Malam Abubakar Jamhuriyar Nijar domin samun ilimin addinin Musulunci, inda ya jaddada cewa shi ne shugaban makarantar firamare ta Tungan Gari da ke karamar hukumar Magama, yana da mata hudu da ‘ya’ya talatin kuma zai ajiye aiki nan da shekaru biyar masu zuwa, shi ne ya sa suka bashi ‘ya’yansu.
Sai dai ya kara da cewa suna biyan dubu 35 ga kowane yaro kowane wata domin su sami damar samun ilimin da ake bukata.
KARSHEN ALIYU LAWA/Wababe
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
Kungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) reshen Jihar Kebbi ta raba kayan abinci da kudi ga iyalan mambobinta da suka rasu a lokacin da suke kan aikin jarida, a matsayin kyautar azumin Ramadan.
Da yake jawabi a wajen taron, Shugaban Kungiyar na Jiha, Kwamared Bello Sarki Abubakar, ya ce suna gudanar da wannan shiri a duk shekara, tun bayan kaddamar da shi da tsohon shugaban kungiyar na jiha Alhaji Aliyu Jajirma ya yi, domin faranta ran iyalan abokan aikinsu da suka rasu.
Kwamared Sarki Abubakar ya bayyana cewa dukkan shugabannin kungiyar da suka gabata sun tabbatar da ci gaba da gudanar da wannan shiri a duk lokacin azumin Ramadan domin rage wa iyalan mamatan radadin wahalhalun rayu.
Ya sanar da cewa kowane iyali daga cikin iyalan mambobi 21 da suka rasu za su karɓi buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 25 da kuma naira dubu goma.
Yayin da yake gode wa Gwamnatin Jihar Kebbi karkashin jagorancin Kwamared Nasiru Idris saboda goyon bayan da take bai wa kungiyar, Kwamared Sarki ya yaba da ayyukan ci gaba da Gwamna Nasir Idris ya aiwatar a cikin shekaru biyu da suka gabata domin inganta rayuwar al’ummar jihar.
Kwamishinan Watsa Labarai da Al’adu na Jihar Kebbi, Alhaji Yakubu Ahmed BK, yayin da yake yaba wa shugabancin kungiyar saboda tallafin da ta bai wa iyalan mamatan, ya tabbatar wa kungiyar cewa Gwamnatin jihar za ta ci gaba da fifita jin daɗin ‘yan jarida a jihar.
Haka kuma, ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don tabbatar da cewa badi an gudanar da wannan taro cikin gagarumin shiri domin faranta wa iyalan mamatan rai.
A madadin wadanda suka ci gajiyar tallafin, daya daga cikin matan wadanda suka rasu, Hajiya Hadiza Abdullahi, ta gode wa kungiyar saboda tunawa da su bayan rasuwar mazajensu.
Daga Abdullahi Tukur