Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-04-13@11:03:29 GMT

PCN Ta Kai Ziyara Ga Hukumar Samarda Magunguna Ta Jihar Kano

Published: 6th, February 2025 GMT

PCN Ta Kai Ziyara Ga Hukumar Samarda Magunguna Ta Jihar Kano

Hukumar Kula da Magunguna ta Najeriya (PCN) ofishin Kano ta kai ziyarar gani da ido ga hukumar samar da magunguna ta jihar Kano (DMCSA).

 

Wannan ziyarar alama ce ta farkon tsarin ba da izini ga DMCSA don zama cibiyar rarraba magunguna ta mega da cibiyar bada horo.

 

Jami’ar Jihar Kano mai kula da ofishin PCN Kano Pharmacist Hasiya Abubakar Ladan ce ta jagoranci tawagar da suka kai ziyarar.

 

Wannan ziyarar wani mafari ne na tantancewa da wata tawagar kwararru daga hedikwatar PCN ta kasa da ke Abuja.

 

Ta bayyana cewa ziyarar na da nufin tantance yadda DMCSA ke bin ka’idoji, don ba da Takaddar Rijistar wuraren sayarda magunguna.

 

Pharmacist Ladan ta yabawa shugabannin DMCSA bisa yadda suke tafiyar da ayyukan kungiyar yadda ya kamata tare da nuna gamsuwa da matakin da hukumar ta dauka.

 

Darakta Janar na DMCSA Pharmacist Gali Sule, ya tarbi tawagar inda ya zagaya da su a rumbunan adana kayayyaki.

 

Ya bayyana cewa hukumar ta dakatar da samar da magunguna domin inganta sashin sarrafa magunguna kamar yadda PCN da NAFDAC suka bada shawara.

 

Pharmacist Sule ta godewa tawagar bisa ziyarar da suka kai tare da ba su tabbacin hadin kan DMCSA a duk lokacin da ake gudanar da aikin tantancewa.

 

KHADIJAH ALIYU/Wababe

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Tantancewa

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu

Shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran ya ce kasashen wamma suna son kebe kansu da fasahar nukliya a tsakaninsu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Muhammad Eslamu shugaban hukumar AEOI yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kafa a kasar Iran kuma ba wanda ya isa ya kauda shi. Sabanin abinda kasashen yamma suke so na hana sauran kasashen duniya mallaka fasahar nukliya, da kuma dogara da su kadai, su bada abinda suka ga dama ko  su hana gaba daya.

Ya ce JMI ta wuce wasu kasashen yamma a ayyuka da kuma sani da sarrafa makamashin Uranium, wanda ya tada hankalin wadannan kasashe, kuma suke sun han awasu kasashen duniya bin sawun kasar Iran na zama yentattu a wannan fage.

Islami ya kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kai wani matsayinda yana taiamakawa sauran kamfanoni na cikin gida ba tare da bukatar dogaro da kwararru ko kuma taimakon kasashen waje ba. Ya ce a halin yanzu iran na samar da wutan lantarki mai karfin magewats 20,000 tare da Makamashin Nukliya.

     

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari
  • Sanƙarau: An tabbatar da ɓullar cutar ga mutane 300 a Sokoto
  • Ruwan Sama Ya Lalata Gidaje Sama Da 240 A Kebbi
  • Mai damfarar fursunoni ya gurfana a kotu a Kano
  • ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja
  • Hisbah ta warware rigingimu 565 da lalata katan 51 na barasa a Yobe
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta