Sarki Sanusi ya ziyarci Rimin Zakara, ya yi kira da a kwantar da hankula kan rikicin filaye
Published: 6th, February 2025 GMT
Mai martaba Sarkin Kano na 16, Muhammadu Sanusi II, ya yi kira da a zaman lafiya da hakuri a tsakanin al’ummar garin Rimin Zakara sakamakon rikicin filaye da ya barke tsakanin al’umma da Jami’ar Bayero ta Kano (BUK).
Sarkin ya yi wannan roko ne a ziyarar da ya kai yankin bayan dawowarsa daga aikin hajji.
Da yake jawabi ga al’ummar yankin, Sarkin ya jajantawa iyalan wadanda suka rasa rayukansu a rikicin tare da addu’ar Allah ya jikan wadanda suka jikkata cikin gaggawa.
“Dole ne mu yi wa wadanda suka rasu addu’a da kuma baiwa iyalansu ikon jure wannan rashi, Allah ya sa wannan ya zama na karshe a cikin irin wannan mummunan lamari a cikin al’ummarmu,” inji shi.
Sarkin ya bukaci mazauna yankin da su kasance masu kamun kai tare da ba da damar bin doka da oda, yana mai jaddada cewa tashin hankali yana haifar da karin wahala ne kawai.
“Lokacin da tashin hankali ya barke mutanenmu ne ke shan wahala, babu wani barna ko zubar da jini da zai magance matsalar, dole ne mu hada kai domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma,” in ji shi.
Da yake la’akari da sarkakiyar rigimar da aka kwashe shekaru ana yi, Sarkin ya bayyana cewa al’umma da jami’a suna da’awar mallakar fili a bisa doka. Ya jaddada bukatar a samar da shawarwari ta hanyar kotu da kuma tattaunawa tare da hukumomin da abin ya shafa.
“Bai kamata wannan al’amari ya kasance mai sarkakiya ba, idan har shari’ar ta kasance a gaban kotu, dole ne a warware ta da kwararan hujjoji, dole ne mu zauna da dukkan bangarorin da abin ya shafa domin samun maslaha mai dorewa,” inji shi.
Domin samar da zaman lafiya, Sarkin ya bayyana shirin kafa wani kwamiti da zai kunshi wakilai daga dukkan masu ruwa da tsaki, da suka hada da gwamnatin jihar, da hukumomin BUK, da hukumomin tsaro, da shugabannin al’umma, domin magance matsalar.
“Za mu hada hannu da Gwamna, da hukumomin BUK, da jami’an tsaro don tabbatar da an yi adalci, amma idan kun sayar da filayen ku, kun karbi diyya, to ku amince da gaskiyar lamarin,” in ji shi.
Sarkin ya kammala ziyarar tasa inda ya bukaci mazauna yankin da su baiwa zaman lafiya da hadin kai fifiko, yana mai jaddada cewa babu wata kasa ko dukiya da ta kai asarar rayukan bil’adama.
“Rayuwar mutum daya ta fi duk duniya daraja, dole ne mu hada kai don ganin ba a sake samun irin wannan bala’i ba, adalci zai yi nasara, kuma Allah yana tare da masu tsayawa kan gaskiya.”
ABDULLAHI JALALUDDEEN KANO
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Sarki
এছাড়াও পড়ুন:
Dole Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Ta Daina Barazana Ga Masu Sukar Ta – Amnesty
Kungiyar ta ce a maimakon neman cin mutuncin Uguamaye kamata ya yi gwamnatin tarayya ta dukufa neman kawo sauyin da zai rage wa jama’a wahalhalun da suke fuskanta da magance matsalolin tattalin arziki da kasar ke ciki.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp