Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-02-22@06:20:19 GMT

‘Yan Sanda Sun Mika Bakin Haure 165  A Birnin Kebbi

Published: 6th, February 2025 GMT

‘Yan Sanda Sun Mika Bakin Haure 165  A Birnin Kebbi

Rundunar ‘yan sandan jihar Kebbi, ta kama wasu bakin haure 165 da aka ce sun fito ne daga kasashen da ke amfani da harshen Faransanci tare da mika su ga hukumar kula da shige da fice ta kasa dake jihar domin gudanar da bincike.

 

A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, SP Nafiu Abubakar ya fitar kuma ya mika wa gidan rediyon Najeriya a jihar Kebbi, ya ce, bisa rahoton bayanan sirri, an gano sama da mutum dari biyu a wani gida mai dakuna uku da ke unguwar Kuwait a cikin birnin Birnin Kebbi.

 

Sanarwar ta ce, tawagar jami’an ‘yan sanda da ke sashin binciken manyan laifuka (SCID) ne suka kai samame unguwar inda suka yi nasarar cafke mutane dari da sittin da biyar (165).

 

Ya bayyana cewa, yayin da ake gudanar da bincike, an gano cewa, dukkan wadanda ake zargin sun fito ne daga kasashen da Faransa ta yiwa mulkin mallaka da suka hada da Burkina Faso, Jamhuriyar Benin, Jamhuriyar Nijar, Mali da Ivory Coast.

 

A cewar sanarwar, bincike ya kara nuna cewa, wadanda ake zargin suna zaune ne a Najeriya ba tare da wasu takardu masu inganci ba kuma ana zarginsu da hannu a cikin shirin Qnet Ponzi.

 

Sanarwar ta ce, bayan kammala binciken farko da rundunar ta gudanar, an mika wadanda ake zargin bakin haure zuwa hukumar shige da fice ta kasa reshen jihar Kebbi, domin ci gaba da bincike da kuma daukar matakin da ya dace.

 

PR/ Abdullahi Tukur

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Dauki Nauyin Dalibai 80 Da Ke Manyan Makarantu

Karamar hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa ta ce za ta dauki nauyin dalibai ‘yan asalin yankin su 80 da ke kwalejin Ilmi ta tarayya ta Jama’are a Jihar Bauchi, da kwalejin fasaha ta Dutse da kuma kwalejin fasahar sadarwa ta Kazaure.

Shugaban Karamar Hukumar, Dr. Muhammed Uba Builder ya bayyana haka ga manema labarai a Birnin Kudu.

Dr Muhammad Uba, yayi bayanin cewar, an zabo mutum uku-uku daga kowace mazaba goma sha daya dake yankin.

Yana mai cewar, Karamar Hukumar ta yanke shawarar hakan ne domin bai wa dalibai damar karatu cikin sukuni.

Dr Muhammad Uba Builder, ya kara da cewar nan gaba kadan Karamar Hukumar za ta kara zabo wasu daliban dan tafiya manyan jami’o’i dake kasar nan.

A cewarsa, an kafa kwamati dan tantancewa daliban da suka cancanta.

A nasa jawabin Shugaban kwamatin tantance daliban kuma shugaban ma’aikata na yankin Yarima Musa, ya ce za su zabo daliban da suka cancata domin tura su makarantun da suka dace.

Ya kuma ya yabawa Shugaban Karamar Hukumar ta Birnin Kudu bisa namijin kokarinsa wajen daukar nauyin karatun daliban domin samun ingantacciyar rayuwa mai amfani a nan gaba.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Dauki Nauyin Dalibai 80 Da Ke Manyan Makarantu
  • Zaɓen ƙananan hukumomin Osun na nan daram – Gwamna Adeleke
  • ’Yan sanda sun daƙile satar mutane, sun kama wasu 3 a Borno
  • Hamas Ta Mika Gawawwakin ‘Yan Isra’ila Hudu Ga Kungiyar Red Cross
  • Na yi nadamar soke zaɓen 1993 — Babangida
  • Harin ’Yan bindiga: Mun yi asarar shanu sama da miliyan 4 – Miyetti Allah
  • Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.
  • Hamas: Za A Mika Gawawwakin ‘Yan Mamaya Da Kuma Fursunoni Rayayyu A Ranakun Alhamis Da Asabar
  • Sojojin Sudan Sun Killace Fadar Shugaban Kasa Da Take A Hannun ‘Yan Tawayen A Birnin Khartum
  • USAID: Amurka za ta yi bincike kan ɗaukar nauyin Boko Haram