Aminiya:
2025-02-22@06:32:19 GMT

Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai

Published: 6th, February 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya goyi bayan Hajiya Naja’atu Muhammad a rikicinta da Mashawarcin Shugaban Kasa kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu.

Rikicin ya kunno kai ne bayan Naja’atu ta bulla a wani bidiyo inda take kushe Nuhu Ribadu ads aiki a gwamantin Tinubu alhali a lokacin da yake Shugaban Hukumar Yaki da Masu Karya Tattalin Arzikin Kasa (EFCC), ya soki Tinubu da zargin sa da almundahana a yayin taron Majalisar Zartaswa ta Kasa (FEC).

Bayan haka ne Ribadu ta hannun lauyansa Ahmed Raji (SAN), ya bukaci ta janye kalaman nata tare da neman afuwarsa, yana mai barazanar maka ta kotu idan ba ta janye ba, domin kalaman nata na neman zubar masa da kima.

Amma duka da haka, Naja’atu, wadda tsohuwar Kwamishina ce a Hukumar Kula da Aikin Dan Sanda (PSC) ta tsaya kai da fata, cewa ba za ta janye ba ballanta na da ba da hakuri.

NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata Ɗan sanda ya harbe kansa har lahira a Nasarawa Gobara ta yi ajalin almajirai 17 a Zamfara
Naja’atu ta kara da cewa a shirye take, ko Kotun Duniya zai kai ta, domin tana da kwararan hujjoji da za ta kare abin da ta fada.

Ana cikin haka ne, El-Rufai ya bayyana cewa gaskiya ne maganar da Naja’atu game da zargin da Nuhu Ribadu ya yi kan Tinubu gaskiya ne.

El-Rufai a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta ya bayyana cewa yana nan Ribadu ya yi wadannan kalamai a taron FEC, lokacin shi El-Rufai yana Ministan Abuja.

Ya ce da alama “Nuhu na fama da matsanciyar cutar matuwa,” inda ya kara da cewa akwai rubutattun hujjoji da ke tabbatar da kalaman Naja’atu, ciki har da takardun Majalisar Dattawa a shekarar 2006.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)

Annabi (SAW) yana da Alfadarai Bakwai, akwai wazanda ya rike har ya rasu suna wurinsa akwai kuma wazanda ya bai wa wasu daga cikin sahabbansa. Wacce ya je yakin Hunaini da ita, wani sarkin Larabawa (zan makafatul kinani) ne ya bashi, akwai wacce sarkin Ailatu ya bashi akwai ta sarkin Limatul Jandali, akwai ta Sarki Najjashi, akwai ta sarkin Kisra, akwai ta sarkin Mukaukisu akwai Jindilu. Jindilu itace mashhuriya wacce Annabi ya rasu ya bar ta Sayyidina Aliyu ya ci gaba da hawanta, duk yakukuwan Sayyidina Ali, mafi yawancinsu a kanta ya yi, ranar yakin Wak’atu Jamal, Sayyada A’isha (RA) ta ganshi a kanta, sai ta ce “ya yi kama da zan’uwansa” sai mai rike da akalar rakuminta ya jefar ya koma cikin rundunar Sayyadina Ali ya ce masa, Sayyada tace “ka yi kama da zan’uwanka (Sayyadina Rasulallah).

Imam Muslim ya ruwaito Hadisi daga Abbas yana cewa “yayin da tawagar Musulmai da Kafirai suka hazu, sai Musulmai suka gudu suka juya baya, sai Manzon Allah shi kuma ya kasance yana jan alfadarinsa inda Kafiran suke, ni kuma ina rike da linzamin alfadarinsa ina jan linzamin baya shi kuma Abu Sufyan zan Haris zan Abdulmuzallib yana rike da wurin sanya kafafuwa na shimfizar alfadarin, sannan Annabi (SAW) ya yi kira ga Musulmai suka dawo.” A wata ruwaya kuma, Annabi (SAW), Baffansa Abbas ya sa ya kira Musulmai.

Annabi (SAW) ya kasance idan ya yi fushi (shi kuma ba ya fushi sai in an taba Allah), to wani abu bai iya tare shi, ko Sahabi ko tsoro ko wata razana.

Abdullahi zan Umar ya ce, “ban taba ganin wani abu mafi sadaukantaka ko karfin zuciya ko kyauta mafi yarda wanda ya fi Annabi (SAW) ba.”

Sayyadina Ali yana cewa “Mun kasance in yaki ya yi zafi, ya yi tsanani idanuwa suka sauya kala suka yi ja, sai mu dinga kare kanmu da Annabi (SAW), babu wani da yake kusantar makiya sai shi, sannan mu biyo bayansa.

An karbo Hadisi daga Anas yana cewa “Manzon Allah (SAW) ya kasance mafi kyawun Mutane, mafi kyautar mutane, mafi sadaukantakar mutane.”

Wata rana da dare mutanen Madina sun razana sabida kara mai karfi da aka ji ta taso a daren, Sahabbai suka fara bi gida-gida suna taso abokansu a je a duba sabida a san me ke faruwa. Kawai sai suka hazu da Manzon Allah (SAW) yana dawowa, ya riga su zuwa wurin, sabida sauri a dokin Abi Dalhata ya je kuma babu shimfiza a kan dokin, yana rataye da takobi yana cewa Sahabbai “kar ku tsorata, na je na gani babu komai.”

A wannan lokaci Madina ta kasance kullum ana tsoron wani daga cikin Sarakunan makiya zai kawo hari.

Imran bin Hussaini yake cewa, Manzon Allah (SAW) bai taba hazuwa da wata runduna ba sai ya kasance na farko wanda zai fara kai musu hari.

Yayin da Ubayyu bin Khalaf ya ga Annabi (SAW) a ranar yakin Uhudu, Ubayyu ya fito yana cewa, Ina Muhammadu yau sai zaya ya mutu a cikinmu, ko ni ko shi. Ubayyu yana daga cikin wazanda suka fanshi kansu a ranar yakin Badr, bayan ya fanshi kanshi sai ya ce wa Annabi (SAW), yana da doki da ya kulle kullum yana bashi masaki na dawa, a kansa zan kashe ka, sai Manzon Allah (SAW) ya ce masa, Insha Allah, ni ne zan kashe ka a kanshi. A ranar yakin Uhudu da Ubayyu ya ga Annabi (SAW), sai ya sukwano dokinshi zuwa ga Annabi (SAW), Mazaje sadaukai suka yi kanshi sai (SAW) ya ce musu “ku kyale shi haka nake so”. Sai Manzon Allah (SAW) ya karbi wani mashi a hannun wani sahabi sannan ya soke shi a wuya daga kan dokinshi, sai ya koma yana ce wa kuraishawa, Muhammadu ya kashe ni, an ruwaito cewa, Ubayyu ya Mutu a hanyar dawowarsa daga Uhudu zuwa Makkah.

Kunya Da Kawar Da Kai Na Manzon Allah (SAW)

Wannan kazan kenan daga cikin sadaukantaka irin ta Annabi (SAW), yanzun kuma za mu juya akalar karatunmu zuwa ambaton wasu daga cikin halayen Kunya da kawar da kai na Manzon Allah (SAW).

Abin da ake nufi da kunya shi ne taushin zuciya da yake bijirowa a fuskar zan Adam yayin da mutum ya aikata wani aiki ko ya faza wata magana da ake kin ji ko gani, ko kuma mutum ya aika ta abin da rashin aikata shi ya fi, sai zan Adam ya ce “ina ma na bari ban aikata ba.”

Shi kuma runtse ido ko kawar da kai, yana nufin rafkana da abin da mutum ba ya so a aikata masa (ba ya so a aikata masa wani abu, ga kuma wani ya nace sai ya aikata abin da ba a son) shi kuma sai ya kawar da kai ya nuna bai san ma ana yi ba.

Manzon Allah (SAW) ya fi kowa Kunya sabida Hadisin “Alhaya’u minal Iman… – Kunya tana daga cikin Imani”.

Manzon Allah (SAW) yana cewa, “wanda bai da kunya, ya aikata abin da ya ga dama, Allah ba ruwanshi da shi”. Annabi (SAW) shi ne mafi kawar da kai ga Al’aurar Mutane.

Ubangiji tabaraka wata’ala ya faza cikin kur’ani “Ya ayyuhallazina amanu la tadkhulu buyutan nabiyya illa an yu’uzana lakum ila za’amin gaira nazirina inahu…”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Thomas Friedman: Trump Yana Son Ci Gaba Da Zama Shugaban Kasar Amurka Har Abada
  • Sadaukantaka, Kunya Da Kawar Da Kai Na Annabi Muhammadu (SAW)
  • Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah
  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa
  • Babban Kwamandan IRGC Ya Bayyana Cewa: Amurka Da Isra’ila Ba Su Yi Nasara A Yakin Gaza Ba
  • Babban Jami’i A Kungiyar JIhadul-Islami Ya Ce: Gudumawar Marigayi Sayyid Hasan Nasrullahi Ba Zai Fadu Ba
  • Shugaba Tinubu Ya Yaba Da Gudunmawar Da IBB Ya Bayar Yayin Mulkinsa
  • Majalisa ta fara bincike kan zargin USAID na tallafa wa Boko Haram
  • Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
  • Tinubu Ya Taya Babban Mai Tace Labarai Na LEADERSHIP, Ishiekwene Murnar Cika Shekaru 60