Aminiya:
2025-03-31@12:41:20 GMT

Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai

Published: 6th, February 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya goyi bayan Hajiya Naja’atu Muhammad a rikicinta da Mashawarcin Shugaban Kasa kan Sha’anin Tsaro, Nuhu Ribadu.

Rikicin ya kunno kai ne bayan Naja’atu ta bulla a wani bidiyo inda take kushe Nuhu Ribadu ads aiki a gwamantin Tinubu alhali a lokacin da yake Shugaban Hukumar Yaki da Masu Karya Tattalin Arzikin Kasa (EFCC), ya soki Tinubu da zargin sa da almundahana a yayin taron Majalisar Zartaswa ta Kasa (FEC).

Bayan haka ne Ribadu ta hannun lauyansa Ahmed Raji (SAN), ya bukaci ta janye kalaman nata tare da neman afuwarsa, yana mai barazanar maka ta kotu idan ba ta janye ba, domin kalaman nata na neman zubar masa da kima.

Amma duka da haka, Naja’atu, wadda tsohuwar Kwamishina ce a Hukumar Kula da Aikin Dan Sanda (PSC) ta tsaya kai da fata, cewa ba za ta janye ba ballanta na da ba da hakuri.

NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata Ɗan sanda ya harbe kansa har lahira a Nasarawa Gobara ta yi ajalin almajirai 17 a Zamfara
Naja’atu ta kara da cewa a shirye take, ko Kotun Duniya zai kai ta, domin tana da kwararan hujjoji da za ta kare abin da ta fada.

Ana cikin haka ne, El-Rufai ya bayyana cewa gaskiya ne maganar da Naja’atu game da zargin da Nuhu Ribadu ya yi kan Tinubu gaskiya ne.

El-Rufai a wani sako da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta ya bayyana cewa yana nan Ribadu ya yi wadannan kalamai a taron FEC, lokacin shi El-Rufai yana Ministan Abuja.

Ya ce da alama “Nuhu na fama da matsanciyar cutar matuwa,” inda ya kara da cewa akwai rubutattun hujjoji da ke tabbatar da kalaman Naja’atu, ciki har da takardun Majalisar Dattawa a shekarar 2006.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce Amurka na da hannu a ayyukan haramtacciyar kasar Isra’ila na yada rashin tsaro da zaman lafiya a yankin.

A wata ganawa da ya yi da Hans Grundberg, wakilin Majalisar Dinkin Duniya na musamman a kasar Yemen a birnin Tehran, Araghchi ya yi Allah wadai da ci gaba da hare-haren soji da Amurka ke kaiwa sassa daban-daban na kasar Yeman, wanda ke sanadin mutuwar fararen hula da kuma lalata kayayyakin more rayuwa.

Ya kara da cewa: Hare-haren da sojojin Amurka suke kai wa kasar Yamen, wanda ya zo daidai da irin yadda gwamnatin sahyoniyawan ke ci gaba da aiwatar da kisan gilla a zirin Gaza da kuma hare-haren da take kaiwa kasashen Lebanon da Siriya, wata alama ce kawai da ke nuna irin hadin kai da Amurka take yi da Isra’ia wajen rashin bin doka da oda da kuma yadda take da alaka da ayyukan Isra’ila wajen yada rashin tsaro da zaman lafiya a yankin.

Ya bayyana cewa Amurka tana da rashin fahimtar mutanen Yemen, wanda kuma yana da kyau ‘yan siyasar Amurka da su gane cewa ci gaba da mamaye da kisan kiyashi a Falasdinu shine tushen rashin tsaro a yankin.

Dole ‘yan siyasar Amurka su fahimci cewa Amurka ba za su  iya da’awar maido da kwanciyar hankali a yankin ba ta hanyar kai hari kan Yemen da kashe mutanen Yemen da ba su ji ba ba su gani ba,” in ji Araghchi.

Ya kara da cewa laifin al’ummar kasar Yaman shi ne hadin kai da goyon bayansu ga al’ummar Palastinu da ake zalunta.

Babban jami’in diflomasiyyar na Iran ya soki kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya da kin daukar wani mataki dangane da keta ka’idojin yarjejeniyar MDD da kuma dokokin kasa da kasa da gwamnatocin Amurka da Isra’ila suke yi.

Ya ce ya kamata Majalisar Dinkin Duniya ta dauki matakai cikin gaggawa don kawo karshen karya doka da rashin mutunta ka’idojin kasa da kasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dan shekara 4 ya kira wa mahaifiyarsa ’yan sanda
  • Iran: Amurka ta hada kai da Isra’ila wajen kawo cikas ga harkar tsaro a gabas ta tsakiya
  • Jakadan Kasar Rasha A Saliyu Ya Ce Kasar Rasha Tana Nazarin Yiyuwar Fara Hakar Ma’adinin bauxite A Kasar
  • Abin da ya sa nake jin daɗin yadda Tinubu yake tafiyar da gwamnatinsa — Buhari
  • Mai Bawa Jagora Shawara Ya Ce ‘Wa’adussadik Na III” Na Kan HKI Na Hanya
  • Wike Ya Jinjina Wa Tinubu kan Bunkasa Ilimi Mai Zurfi
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [21]
  • Tinubu Ya Ba Da Umarnin Kamo Waɗanda Suka Kashe ‘Yan Arewa A Edo
  • Ribas: Ƙungiyar Ƙwadago Na Barazanar Shiga Yajin Aiki In Har Ba A Janye Dokar Ta-ɓaci Ba
  • ‘Yansanda Sun Hana Hawan Sallah A Kano Saboda Tsaro