Aminiya:
2025-04-28@02:36:31 GMT

An kashe wa ma’aurata ’ya’yansu uku a boye gawarsu a firinji

Published: 6th, February 2025 GMT

Wasu ma’aurata sun tsinci gawarwakin kananan ’ya’yansu uku a boye a cikin wani firinji a yankin Nnewichi da ke Nnewi a Jihar Anambra.

Iyayen yaran, Mista Udochukwu da Misis Chikazor Ejezie, sun tsinci gawar ’ya’yan nasu a cikin firinji ne bayan da suka dawo gida daga wurin aiki.

Bayan dawowarsu ne suka samu gidan a bude ba yadda suka saba ba, kasancewar yaran suka kulle gidan a duk lokacin da za su je wasa.

Da shigarma’auratan cikin gidan ne kuma suka ga gawarwakin yaran an sanya a cikin firinjin kayan kankara.

Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata Kotu ta ɗaure Farfesa shekara 3 kan aikata maguɗin zaɓe

Lamarin da ya faru a karshen mako ya tayar da kura, musamman a kafofin sada zumunta.

Bayan hakan ne gwamnatin jihar ta yi alkawarin bin diddigi tare da kama masu hannu a wannan aika-aika.

A yayin ziyarar da ta kai wurin, Kwamishinar Harkokin Mata da Walwalar Jama’a, Misis Ify Obinabo, ta ba da tabbacin yin duk mai yiwuwa wajen ganin an yi wa yaran adalci.

Kwamishinar, ta kuma jaddada haka a lokacin da ta ziyarci Asibitin Koyarwa na Jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke Nnewi, inda aka ajiye gawarwakin yaran.

Mazauna unguwar sun bayyana lamarin a matsayin babban tashin hankali a yayin da suke ta tausaya wa ma’auratan.

Tuni dai hukumomin jihar Anambra suka kaddamar da bincike kan lamarin da nufi lalubo bakin zaren.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Anambra kananan yara yara

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Gargadin Munanan Sakamakon Da Zai Biyo Bayan Kashe Falasdinawa

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran yayi kashedin kan illar ci gaba da killace Gaza da kuma hare-haren ta’addancin ‘yan mamaya

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Ci gaba da rashin hukunta ‘yan sahayoniyya kan kisan gillar da suke yi a zirin Gaza da Gabar yammacin kogin Jordan, da kuma mamayar wasu yankunan kasar Labanon da Siriya yana da matukar barazana ga zaman lafiya da tsaro a yankin.

A cikin wata sanarwa da ya fitar a yau Juma’a, Isma’il Baqa’i ya yi kakkausar suka kan ci gaba da ayyukan wuce gona da iri da na ta’addancin yahudawan sahayoniyya a Gaza da Lebanon.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa
  • An kashe sojoji 12 a barikin Nijar
  •  Nigeria: Boko Haram Ta Kashe Mutane 12 A Borno
  • Me Ke Sa Amare Yin Watsi Da Kwalliya Idan Sun Kwana Biyu A Gidan Miji?
  • ’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno
  • Boko Haram Sun Kashe Mutum 12 A Wani Sabon Hari A Borno
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’dda 1,770 sun kama 3,070 a Arewa —Janar Musa
  • Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Yi Gargadin Munanan Sakamakon Da Zai Biyo Bayan Kashe Falasdinawa
  • Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe
  • Tuƙin Ganganci: Direba Ya Kashe Jami’in KAROTA