MDD Ta Yi Gargadi Akan Halin Da Ake Ciki A DRC
Published: 6th, February 2025 GMT
Kungiyar M 23 mai samun goyon bayan Rwanda ta kara samun gindin zama a gabashin kasar DRC, duk da cewa ta sanar da tsagaita wutar yaki ta gefe daya a jiya Laraba.
Mayakan na M 23 sun sanar da kame babban binin gundumar Bukavu.
Wani jami’in MDD wanda ya isa garin Goma ya bayyana cewa, Da akwai yiyuwar barkewar wani sabon rikici.
MDD ta ce har yanzu ana ci gaba da yaki tsakanin sojojin gwamnati da kuma mayakin na kungiyar M 23.
Garin Goma da mayakan na M 23 su ka kwace iko da shi, yana da ma’adanai kwance a kasansa da aka yi kirdadon cewa kudadensa sun kai na biliyoyin daloli.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Jagora Ya Gana Da Shuwagabannin Kungiyar Jihadul Islami A Nan Tehran
Jagoran juyin juya halin Musulunci A nan Iran Imam Sayyid Aliyul Khaminae ya gana da shuwagabannin kungiyar Jihadul Islami na kasar Falasdinu da aka mamaye a jiya Talata.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya bayyana cewa Ziyad Nakhalah shugaban kungiyar ne ya jagoranci tawagar kungiyar zuwa ganawa da jagoran.
Labarin ya nakalto Jagoran juyin juya halin musulunci ya fadar cewa a halin yanzu babu wani abunda HKI zata yi a gaza sai idan kungiyoyi masu gwagwarmaya suna sun abin ya faru, saboda kekkyawar riko da suka yiwa yankin.
Imam Seyyed Ali Khamenei, ya yabawa kungiyoyin falasdinawa kan hadin kai da suka nuna a yankin da ya gabata.
Ziyad al-Nakhalah, babban sakataren kungiyar Jihad Islami, ya bayyana cewa sun zo gaban Rahbar ne don tattauna mataki nag aba da yakamata su dauka a halin da ake ciki a kasar Falasdinu da aka mamaye.