Aminiya:
2025-03-25@17:55:36 GMT

An kashe wa ma’aurata ’ya’yansu uku an ɓoye gawarsu a firinji

Published: 6th, February 2025 GMT

Wasu ma’aurata sun tsinci gawarwakin kananan ’ya’yansu uku a boye a cikin wani firinji a yankin Nnewichi da ke Nnewi a Jihar Anambra.

Iyayen yaran, Mista Udochukwu da Misis Chikazor Ejezie, sun tsinci gawar ’ya’yan nasu a cikin firinji ne bayan da suka dawo gida daga wurin aiki.

Bayan dawowarsu ne suka samu gidan a bude ba yadda suka saba ba, kasancewar yaran suka kulle gidan a duk lokacin da za su je wasa.

Da shigarma’auratan cikin gidan ne kuma suka ga gawarwakin yaran an sanya a cikin firinjin kayan kankara.

Zargin Tinubu: Gaskiya Naja’atu ta fada kan Nuhu Ribadu —El-Rufai NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata Kotu ta ɗaure Farfesa shekara 3 kan aikata maguɗin zaɓe

Lamarin da ya faru a karshen mako ya tayar da kura, musamman a kafofin sada zumunta.

Bayan hakan ne gwamnatin jihar ta yi alkawarin bin diddigi tare da kama masu hannu a wannan aika-aika.

A yayin ziyarar da ta kai wurin, Kwamishinar Harkokin Mata da Walwalar Jama’a, Misis Ify Obinabo, ta ba da tabbacin yin duk mai yiwuwa wajen ganin an yi wa yaran adalci.

Kwamishinar, ta kuma jaddada haka a lokacin da ta ziyarci Asibitin Koyarwa na Jami’ar Nnamdi Azikiwe da ke Nnewi, inda aka ajiye gawarwakin yaran.

Mazauna unguwar sun bayyana lamarin a matsayin babban tashin hankali a yayin da suke ta tausaya wa ma’auratan.

Tuni dai hukumomin jihar Anambra suka kaddamar da bincike kan lamarin da nufi lalubo bakin zaren.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Anambra kananan yara yara

এছাড়াও পড়ুন:

Karin Sinawa Suna Son Kashe Kudi

A kwanakin baya, bankin Deutsche, banki mafi girma na kasar Jamus ya yi bayani game da yanayin kashe kudi ta kasar Sin cewa, karin Sinawa suna kara son kashe kudi. Bisa sabon rahoton da bankin ya gabatar, an ce, idan aka kwatanta da na shekarar bara, yawan masu kashe kudi na kasar Sin yana karuwa, kashi 52 cikin dari na wadanda suka bayyana ra’ayoyinsu a binciken sun ce suna son kara kashe kudi, adadin da ya kai matsayin koli a shekara daya da ta gabata. Kididdigar da gwamnatin kasar Sin ta gabatar ita ma ta shaida wannan yanayi, a farkon watanni biyu na shekarar bana, yawan kudin kayayyakin da aka sayar a kasar Sin ya kai Yuan triliyan 8 da biliyan 373 da miliyan 100, karuwar da ta zarce zaton da aka yi.

Me ya sa karin Sinawa suke son kashe kudi? Farfesa Wang Xiaosong na kwalejin ilmin tattalin arziki na jami’ar Renmin ta kasar Sin ya yi nuni da cewa, tun daga shekarar bara, tattalin arzikin Sin ya samu karuwa, kudin shiga na jama’ar kasar shi ma ya karu, lamarin da ya zama silan karuwar kudi da ake kashewa. Kana gwamnatin kasar Sin ta gabatar da jerin matakan tallafi don sa kaimi ga fadada kashe kudi a kasar.

Kasar Sin tana da mutane fiye da biliyan 1 da miliyan 400, tana daya daga cikin manyan kasuwanni na duniya. Kamfanin McKinsey ya yi hasashen cewa, ya zuwa shekarar 2030, mazaunan biranen kasar Sin za su sa kaimi ga karuwar kashe kudi ta duniya da kashi 91 cikin dari, biranen kasar Sin 700 za su samar da gudummawa ga karuwar kashe kudi na biranen duniya da dala triliyan 7, wanda ya kai kashi 30 cikin dari. Kashe kudi ya sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arziki, ana kara kashe kudi a kasar Sin, babu shakka za a samu sabon karfin raya tattalin arzikin duniya. (Zainab Zhang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fursunoni 12 Sun Tsere Daga Gidan Yari A Jihar Kogi
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  • An kama jarkokin manja maƙare da alburusai a Abuja
  • Fursunoni 12 sun tsere bayan fasa gidan yari a Kogi
  • Gobara ta tashi a gidan mai sakamakon fashewar tanka a Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
  • Karin Sinawa Suna Son Kashe Kudi