Ƴananda Sun Daƙile Yunƙurin Satar Mutane, Sun Kama Ƴan Ta’adda 4 A Kwara
Published: 6th, February 2025 GMT
Rundunar ƴansanda ta jihar Kwara ta daƙile yunƙurin sace mutane biyu tare da cafke mutum huɗu da ake zargi da hannu a lamarin a ƙananan hukumomin Ifelodun da Baruten.
Kakakin rundunar, Toun Ejire-Adeyemi, ya bayyana cewa jami’an tsaro sun cafke su ne bayan bin diddigin kiran wayar barazana da wasu mutane suka samu a Ifelodun da Ilesha-Baruba, inda aka buƙace su biya kuɗin fansa har Naira miliyan tara.
Bincike ya kai ga cafke Umar Sanni daga jihar Neja da Dairu Isiaku daga Ifelodun, da kuma Tukur Muhammad da Yahaya Abdullahi, waɗanda suka amsa laifin yin barazana da ƙoƙarin karɓar kuɗin fansa. An gurfanar da su a kotu, kuma an tura su gidan yari domin ci gaba da shair’a.
কীওয়ার্ড: Kwara
এছাড়াও পড়ুন:
An Bukaci Gwamnati A Kowani Mataki Da Ta Taimakawa Yaki Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
An yi kira ga gwamnati a dukkan matakai da su hada kai da sauran masu ruwa da tsaki a harkar rage karuwar amfani da magungunan ba bias ka’ida ba a tsakanin matasa.
Babban Daraktan Kula da Lafiya (CMD,) a Babban Asibitin Neuro-Psychiatric na Tarayya, Budo Egba, Jihar Kwara, Dokta Issa Awoye, ya yi wannan kiran ne a cikin jawabinsa mai taken, Sakamakon Neuropsychiatric na Maganganun Magani: Ra’ayin Clinical a taron masu ruwa da tsaki na Kwara na biyu kan Kariya da Sarrafa miyagun kwayoyi, wanda aka gudanar a Ilorin.
A cewarsa an samu karuwar noma da fataucin miyagun kwayoyi a kasar, musamman a tsakanin matasa.
Ya jera magungunan da aka saba amfani da su sun hada da tramadol, codein maganin tari syrup, methamphetamine (meth), rohypnol, ecstasy da sauransu.
Dr.Awoye ya ce magungunan galibi suna da rahusa kuma sun fi amfani da su fiye da na gargajiya da ke haifar da babbar illa ga daidaikun mutane.
Ya bayyana cin hanci da rashawa da ke tsakanin jami’an tsaro da na hukumar a matsayin daya daga cikin kalubalen da ke kawo cikas ga kokarin dakile safarar miyagun kwayoyi a kasar.
A nasa jawabin, mataimaki na musamman ga gwamnan jihar Kwara kan yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi, Mukail Aileru, ya ce gwamnatin jihar ta dukufa wajen ganin ta magance matsalar shan muggan kwayoyi.
Ya yi bayanin cewa karuwar tabarbarewar magungunan na haifar da babbar barazana ga lafiyar jama’a, tsaro, da makomar matasa”.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU