HausaTv:
2025-02-22@06:31:53 GMT

Daliban Kasar Bangaladesh Sun Kona Gidan Tsohon Shugaban Kasa

Published: 6th, February 2025 GMT

Rahotanni da suke fitowa daga kasar ta Bangaladesh sun ce, a jiya Laraba da marece ne wasu dalibai da sauran mutanen gari sun ka cinna wuta a cikin gidaje masu yawa, da su ka hada da na tsohon shugaban kasa Mujibur Rahman. Abinda yake faruwa yana nuni ne da dambaruwar siyasa da kasar take ci gaba da fuskanta da kuma rashin gamsuwar da mutanen kasar nunawa akan halin da ake ciki.

Masu bin diddigin abinda yake faruwa a cikin  kasar ta Bangaladesh suna cewa, kai hari a gidan Mujibur Rahman da ake girmamawa a fadin  kasar yana nuni da zurfin matsalar da kasar take ciki. Masu Zanga-zangar suna bayar da taken yin kira ga juyin juya hali a kasar a lokacin da suke yin kone-kone.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu

Shugaban kasar Iran da Sarkin kasar Qatar sun jaddada muhimmancin hadin gwiwa da taimakekkeniya tsakanin kasashen yankin Gabas ta Tsakiya

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian da sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hamid Al Thani sun gudanar da taron manema labarai na hadin gwiwa a birnin Tehran, inda suka jaddada karfin dangantakar da ke tsakanin kasashen biyu, da kuma muhimmancin kara inganta taimakekkeniya a tsakanin kasashensu.

Shugaban na Iran ya fada a yammacin yau Laraba cewa: Ci gaba da tarukan tsakanin jami’an kasashen biyu ke yi na tabbatar da kyakkyawar alakar da ke tsakaninsu, yana mai jaddada karfafa alaka da kasashe makwabta, musamman kasar Qatar, a matsayin wani muhimmin ka’ida na manufofin ketare na Iran.

Shugaban kasar ya ci gaba da cewa: Sun tattauna da Sarkin Qatar kan batutuwan da suka shafi kasashen biyu ta hanyar da za ta tabbatar da moriyar kasashensu, kuma an yanke wasu muhimman shawarwari na raya kasa da zurfafa dangantaka da bude sabbin hanyoyin hadin gwiwa. Sarkin Qatar ya kuma jaddada bukatar samar da sabbin damar gudanar da hadin gwiwa.

Shugaba Pezeshkian ya kara da cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta yi imanin cewa, kasashen yankin suna da karfin daukar matakai na tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin, bisa tushen kyakkyawar makwabtaka da mutunta juna da kyautata mu’amala mai ma’ana, da share fagen kafa wani tsari na hadin gwiwa da taimakekkeniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Thomas Friedman: Trump Yana Son Ci Gaba Da Zama Shugaban Kasar Amurka Har Abada
  • MDD Ta Yi Gargadin Barkewar Yakin Da Zai Hada Kasashe A DRC
  • Jirgin Saman Da Kasar Sin Ta Kera Mai Amfani Da Lantarki Ya Yi Tashin Farko Cikin Nasara
  • Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah
  • Trump Yana Son Ganin Bayan Shugaban Kasar Ukraine Volodimir Zelezky Daga Kujerar Shugabancin Kasarsa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Cewa: Suke Da Hakkin Yanke Shawarar Makomar Kaarsu Ba Amurka Ba
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Shugaban Kasar Iran Ya Tattauna Da Sarkin Kasar Qatar Kan Muhimmancin Hadin Gwiwa Da Taimakekkeniya Tsakaninsu
  • Sojojin Sudan Sun Killace Fadar Shugaban Kasa Da Take A Hannun ‘Yan Tawayen A Birnin Khartum
  • Ma’aikatar sharia ta kasar Iran Ta bada sanarwan Kama Yan Kasar Burtaniya 2 Tare Da Tuhumar Leken Asiri