Aminiya:
2025-04-14@17:37:28 GMT

HOTUNA: Yadda gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a Kano

Published: 6th, February 2025 GMT

Wata gobara da ta tashi a Ƙauyen Zago da ke Ƙaramar Hukumar Danbatta a Jihar Kano, ta ƙone gidaje, amfanin gona, da dabbobi, lamarin da ya janyo wa mazauna ƙauyen asara mai tarin yawa.

Gobarar, ta fara ne da safiyar ranar Laraba, inda ta ƙone gidaje da dama tare da lalata hatsi da sauran amfanin gona.

An yi garkuwa da tsohon Shugaban Hukumar NYSC Janar Tsiga Ɗan firamare ya je makaranta da bindiga yana barazanar harbe ɗalibai

Har ila yau, ta kashe shanu da sauran dabbobi mallakin mazauna ƙauyen.

Wasu daga cikin mazauna ƙauyen, Hayyo Zago da Abdulrahman Zago, sun ce gobarar ta ci gaba da ci har zuwa rana kafin jami’an kashe gobara su iss, inda suka yi nasarar kashe ta.

Da yake tabbatar da aukuwar lamarin, Jami’in Yaɗa Labarai na Yanki, Abdullahi Musa Gyadi-Gyadi, ya ce za a fitar da cikakken bayani kan asarar da aka tafka daga baya.

A nasa ɓangaren, kakakin Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kano, Saminu Yusuf Abdullahi, ya ce har yanzu ba a gano musabbabin tashin gobarar ba.

Amma ana tattara cikakken rahoto kan lamarin.

 

Go hotunan yadda gobarar ta yi ɓarna a ƙauyen:

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Gobara Ƙauye

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum 45 Sun Rasa Rayukansu A Wani Sabon Hari A Filato 

Sai dai har yanzu rundunar ‘yansandan jihar ba ta fitar da wata sanarwa ba kan lamarin, kuma ƙoƙarin da samun martaninsu ya ci tura.

 

A gefe guda kuma, gwamnatin jihar Filato ta nuna damuwa kan hare-haren da ake samu a wasu sassan faɗin jihar, lamarin da ke ƙara haifar da damuwa a zuƙatan jama’a.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Bello Turji ya kashe manoma 11 a Sakkwato
  • Mutum 45 Sun Rasa Rayukansu A Wani Sabon Hari A Filato 
  • An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Ta kai ƙarar kamfanin jirgi da fasinja kan kukan yaro
  • An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
  • Yadda Ake Tuwan Amala Da Miyar Uwaidu
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
  • An kashe mutum kan zargin satar kare a Bauchi