Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa
Published: 6th, February 2025 GMT
A wani rahoto na ibtila’i da ya afku a unguwar Ukubie da ke ƙaramar hukumar Ijaw ta Kudu a Jihar Bayelsa inda wata mata mai suna Madam Stella ta jefa ‘yarta ’yar shekara shida mai suna Rachael a cikin kogi saboda fushi.
A cewar shaidu, Rachael ta je yin wanka a bakin kogi duk da gargaɗin da mahaifiyarta ta yi mata.
“Lokacin da mahaifiyar ta samu ’yarta a bakin kogin, sai ta fusata. Duk da gargaɗin da aka yi mata na ƙauracewa kogin, Rachael ta ƙi, wanda hakan ya sa mahaifiyar tashin hankali ta fusata,” in ji wani ganau.
A cikin fushi, an samu rahoton cewa Madam Stella ta kama hannun Rachael kuma ta jefa ta a cikin wuri mai zurfi a kogin sau biyu, wanda ya kai ga mutuwar ‘yarta.
Bayan faruwar lamarin, jama’ar yankin unguwar da abin ya shafa sun tunkari mahaifiyar, inda ta amsa aikata laifinta, inda ta ce ba ta yi niyyar kashe ɗiyarta ba.
Lamarin da ya jefa jama’ar yankin Ukubie cikin firgici, inda wani ɗan uwansu mai suna Jeph Nation ya bayyana ra’ayinsa.
“Na riga na rasa ‘yan uwa guda biyu a wannan shekara, amma wannan shi ne mafi zafi da ban tausayi,” in ji shi.
Hotunan bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna Madam Stella ta furta wannan iƙirari da yaren ƙabilar Ijaw, inda jama’a suka kewaye ta.
A wani bidiyo, an ganta zaune a cikin kwale-kwale da gawar ɗiyarta a gefenta, tana ɗauke da ita.
A halin da ake ciki, rundunar ‘yan sandan Jihar Bayelsa, ta bakin kakakinta, DSP Musa Mohammed, ya bayyana cewa har yanzu ba a kai ga sanar da rahoton faruwar lamarin ga ‘yan sanda ba a hukumance.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bayelsa Ijaw Mahaifiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kwamishinan ‘Yansandan Kano Ya Nemi Taimakon Sarakunan Gargajiya Wajen Kawo Ƙarshen Faɗan Daba A Jihar
Ya ce sama da mutane 150 ne aka kama da laifin faɗan ɗaba da tashin hankali, tare da ƙwato makamai, miyagun ƙwayoyi da kayan sata.
Ya ƙara da cewa matsalolin faɗan ɗaba da shaye-shaye barazana ce ga zaman lafiyar jama’a da makomar matasa.
Duk da yake kame na da muhimmanci, Bakori ya ce dole ne a bai wa matasa damar samun ilimi, koyon sana’o’i da kuma wasu ayyuka da za su riƙa shagaltar da su zuwa hanya mafi dacewa.
Ya kuma shawarci shugabannin ‘yansanda na ƙananan hukumomi da su riƙa haɗa kai da sarakunan gargajiya da al’ummar yankinsu wajen gano matsalolin tsaro a yankunansu.
“Idan muka haɗa kai da goyon bayan jama’a, babu yadda ‘yan daba za su ci gaba da addabar Kano,” in ji CP Bakori.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp