Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa
Published: 6th, February 2025 GMT
A wani rahoto na ibtila’i da ya afku a unguwar Ukubie da ke ƙaramar hukumar Ijaw ta Kudu a Jihar Bayelsa inda wata mata mai suna Madam Stella ta jefa ‘yarta ’yar shekara shida mai suna Rachael a cikin kogi saboda fushi.
A cewar shaidu, Rachael ta je yin wanka a bakin kogi duk da gargaɗin da mahaifiyarta ta yi mata.
“Lokacin da mahaifiyar ta samu ’yarta a bakin kogin, sai ta fusata. Duk da gargaɗin da aka yi mata na ƙauracewa kogin, Rachael ta ƙi, wanda hakan ya sa mahaifiyar tashin hankali ta fusata,” in ji wani ganau.
A cikin fushi, an samu rahoton cewa Madam Stella ta kama hannun Rachael kuma ta jefa ta a cikin wuri mai zurfi a kogin sau biyu, wanda ya kai ga mutuwar ‘yarta.
Bayan faruwar lamarin, jama’ar yankin unguwar da abin ya shafa sun tunkari mahaifiyar, inda ta amsa aikata laifinta, inda ta ce ba ta yi niyyar kashe ɗiyarta ba.
Lamarin da ya jefa jama’ar yankin Ukubie cikin firgici, inda wani ɗan uwansu mai suna Jeph Nation ya bayyana ra’ayinsa.
“Na riga na rasa ‘yan uwa guda biyu a wannan shekara, amma wannan shi ne mafi zafi da ban tausayi,” in ji shi.
Hotunan bidiyo da ke yawo a shafukan sada zumunta sun nuna Madam Stella ta furta wannan iƙirari da yaren ƙabilar Ijaw, inda jama’a suka kewaye ta.
A wani bidiyo, an ganta zaune a cikin kwale-kwale da gawar ɗiyarta a gefenta, tana ɗauke da ita.
A halin da ake ciki, rundunar ‘yan sandan Jihar Bayelsa, ta bakin kakakinta, DSP Musa Mohammed, ya bayyana cewa har yanzu ba a kai ga sanar da rahoton faruwar lamarin ga ‘yan sanda ba a hukumance.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bayelsa Ijaw Mahaifiya
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila ta kashe wani mamba na ofishin siyasa na Hamas
Wani sabon kazamin harin sojojin Isra’ila ya yi sanadin shahadar mutum 40 cikin sa’o’I 24 da suka gabata ciki har da Salah al-Bardawil, dan majalisar Falasdinu kuma mamba a ofishin siyasa na kungiyar gwagwarmaya ta Hamas.
A cikin wata sanarwa da ta fitar yau, Hamas ta ce an kai wa Bardawil hari ne a wani hari na ” yahudawan sahyoniya na ha’inci”, a lokacin da yake gudanar da sallar dare a daren 23 ga watan Ramadan.
An kashe shi ne tare da matarsa a wani hari da Isra’ila ta kai ta sama a kan tantinsa da ke yankin al-Mawasi, yammacin birnin Khan Yunis na kudancin Gaza.
Kungiyar ta bayyana Bardawil a matsayin “alama ta siyasa, yada labarai,” da ayyukan bunkasa al’umma da yankin Falastinu.
Isra’ila ta kaddamar da yakin kisan kare dangi a Gaza a ranar 7 ga Oktoba, 2023, amma ta kasa cimma manufofinta duk da kashe Falasdinawa 49,747, galibi mata da kananan yara, tare da jikkata wasu fiye da 113,213 a yankin da aka yi wa kawanya.