Tinubu ya sauke shugabar Jami’ar Abuja, ya yi sauye-sauye a jami’o’in Najeriya
Published: 6th, February 2025 GMT
Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu ya sauke Aisha Maikudi daga muƙaminta na Shugabar Jami’ar Abuja, wadda yanzu ake kira da Jami’ar Yakubu Gowon.
Sanarwar sauke Maikudi ta fito ne jim kaɗan bayan ta jagoranci bikin maraba da sabbin ɗalibai a jami’ar.
Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa HOTUNA: Yadda gobara ta ƙone gidaje, amfanin gona da dabbobi a KanoTun farko, naɗinta ya jawo ce-ce-ku-ce, inda wasu malaman jami’ar suka ce ba ta cancanta ta riƙe wannan matsayi bisa doka.
Tinubu ya naɗa Farfesa Lar Patricia Manko a matsayin Muƙaddashiyar Shugabar Jami’ar na tsawon watanni shida.
Sai dai ba za ta iya neman kujerar dindindin ba idan aka buɗe damar neman muƙamin.
Cikakken bayani na tafe…
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Jami ar Abuja Jami ar Yakubu Gowon Kora
এছাড়াও পড়ুন:
Wani Bawan Allah Ya Rasu Jim Kadan Bayan Sallar Asuba A Wani Masallaci A Abuja
Ya ce, “Da misalin karfe 7:28 na safe ne wasu da ke sharar masallacin suka ga mutumin a kwance a cikin masallacin, sai suka yi kokarin tayar da shi domin su yi shara amma shiru.
Nan da nan, sai mutanen suka sanar da Musulman yankin lamarin, inda suka garzaya da shi zuwa asibiti, likitan da ke bakin aiki ya tabbatar da rasuwarsa.
Musa ya ce, daga bisani aka mika gawar marigayin ga ‘yan uwansa domin yi masa jana’iza.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp