Aminiya:
2025-03-25@20:09:11 GMT

An tsinci gawar Ɗan Majalisar da aka yi garkuwa a jajibirin Kirsimeti

Published: 6th, February 2025 GMT

An tsinci gawar mai shari’a Azuka, Ɗan Majalisa mai wakiltar mazaɓar Onitsha ta Arewa a Majalisar Dokokin Jihar Anambra.

An gano gawar Azuka da aka sace a jajibirin Kirsimeti a shekarar 2024 a kan gadar 2nd Niger Bridge, a cikin Anambra, ranar Alhamis.

Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa Yadda matar aure ta kashe dan kishiyarta da tafasasshen ruwa

Marigayin yana hanyarsa ta zuwa bukukuwan ƙarshen shekara ne tare da ‘yan uwansa a lokacin da ’yan bindiga suka yi awon gaba da shi a Ugwunakpamkpa da ke cikin garin Onitsha.

Sai dai jami’an tsaro da ke binciken sace shi sun cafke wasu da ake zargin sun kai su inda aka gano gawarwakin mambobin jam’iyyar Leba.

Da aka tuntuɓi jami’in hulɗa da jama’a na ’yan sanda a Anambra, SP Tochukwu Ikenga, ya tabbatar da faruwar lamarin.

“Jami’anmu sun gano gawar yanzu. Kuma ina ganin ya kamata su kasance a kan hanyarsu a yanzu su kawo gawar nan (hedkwatar ’yan sandan jihar, Amawbia). Za mu sanar da manema labarai da zarar gawar ta iso nan,” in ji SP Ikenga

Da aka tambaye shi ya ba da cikakken bayani kan yadda aka gano gawar, sai ya ce, “Ina son Kwamishanan ‘yan sanda ya yi magana a kai. Ku jira kawai, zai yi wa manema labarai bayani a kai.”

Azuka shi ne ɗan majalisa a karo na biyu da aka kashe a Anambra a cikin shekaru biyu da suka gabata.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Anambra Majalisar Dokokin Jihar

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda ake noman gurjiya

A tattaunawarsa da Aminiya wani manomin gurjiya, Malam Muhammad Dahiru Kanda ya bayyana cewa, ya shafe sama da shekara 25 yana noman gurjiya ba tare da ya taba samun wani tasgaro ba.

Ya kara da cewa, shi noman gurjiya na da muhimminci matuka domin kuwa yana samar wa duk mai yin sa babbar riba.

Mata sun ƙwace kasuwancin kayan lambu a Gombe Mutumin da girgizar ƙasa ta razana ya shekara 2 yana zaune a cikin kogo

A cewarsa, noman gurjiya noma ne da bai sai ka tanadar masa babbar gona ba, ya danganta ne ga yadda duk ka dauke shi, amma kuma ko da rabin hekta ka dauka, ka noma, matukar ka gyara ta to kuwa ko tantama babu in Allah SWT Ya so za ka same ta a yalwace.

Haka nan in har ya kasance ka samu kasar noma mai kyau kuma mai karfi za ka samu alheri sosai wajen samun biyan bukata.

A cewarsa a duk shekara yakan samu buhunhuna biyar zuwa 7 na gurjiya a ‘yar karamar gonarsa da ba ta kai eka guda ba, wadda wannan gurjiya in ya samu yakan biya bukatunsa da na iyalansa.

Ya ci gaba da cewa, noman gurjiya na bukatar hakuri da kuma shuka ta a kan lokaci daidai da lokacin da aka fara shuka gyada domin kuwa ita gurjiya kamar gyada ce, tana bukatar shiga cikin kasa tunda ‘ya’yanta a cikin kasa take zuba su.

Haka kuma, noman gujiya in son samu ne, ka kebance mata wurinta daban komai kakantarsa, maimakon ka shuka ta cikin gero ko dawa ko kuma hada ta cikin gyada domin in ka kebance wajen shuka ta daban, takan fi haihuwa da yawa sabanin shuka ta hade da wasu amfanin gona, kana tana bukatar a dan sa takin gida ko na zamani.

Don haka a gaskiya noman gujiya na da matukar muhimmanci domin kuwa yakan samar wa manoma alherin da ba ya misaltuwa, musamman ganin cewar gurjiya na da matukar daraja a kasuwa.

A yanzu haka buhun gurjiya mai nauyin kilo 50 kudinsa ya kai kimanin Naira dubu 55 zuwa dubu 60.

Baya ga haka kuma akwai bukatar manomi in ya zo shuka gurjiya, ya zabo iri mai kyau ba irin da zai tsumbure ba domin samun yalwarta.

“Yin hakan na daga cikin abin da ke taimaka min da ma sauran manoma wajen samun gurjiya mai yawa in lokacin cire ta ya yi, kuma matukar manomi na son amfana da ita a kaka, to kuwa ya guji yawan cire ta da danyentakarta tun ba ta kai ga kosawa ba, don sayarwa.

Sai dai in ba bukatar hakan ne ta taso ba, domin ni sau tari nakan hakura ne da cirar ta in tana danya illa daga lokaci zuwa lokaci nakan cira don kai wa iyali su dafa, su ci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Masu neman yi wa Natasha kiranye ba su cika ƙa’ida ba — INEC
  • Shugaban Majalisar Dokokin Kasar Lebanon Ya Ce Basa Da Wani Shiri Na Samar Da Haldar Jakadanci Da HKI
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye
  • Sin Ta Sanar Da Dokar Dakile Takunkuman Kasashen Waje
  •  Shugaban Majalisar Dokokin Lebanon Ya Yi Gargadi Akan Masu Tunanin Kulla Alakar Kasar Da HKI
  • Dokar Ta-ɓaci A Ribas: Gwamnonin PDP Sun Ƙalubalanci Hukuncin Tinubu A Kotun Ƙoli
  • Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha
  • Duniya na ci gaba da yin tir da Isra’ila kan dawo da hare-harenta a Gaza
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
  • Yadda ake noman gurjiya