Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai
Published: 6th, February 2025 GMT
Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci hukumomin ilimi su tabbatar da cewa makarantun gwamnati da masu zaman kansu sun ɗauki matakan kare ɗalibai daga haɗura.
Wannan kira na zuwa ne bayan da wata gobara ta yi ajalin almajirai 17 a wata makarantar tsangaya da ke garin Ƙauran Namoda, a Jihar Zamfara.
Allah Ya yi wa Sheikh Ishaq Yunus rasuwa Tinubu ya yi sauye-sauye a Jami’ar AbujaGobarar, wacce ta tashi da daddare a ranar Talata, ta kuma jikkata wasu almajirai bakwai, amma yanzu haka suna asibiti ana kula da su.
Shugaba Tinubu ya jajanta wa Gwamnatin Jihar Zamfara da iyalan waɗanda da suka rasa ’ya’yansu a wannan iftila’in, tare da yin addu’ar samun sauƙi ga waɗanda suka jikkata.
Ya buƙaci makarantu da su fifita tsaro da kula da lafiyar ɗalibai a kowane lokaci.
A yayin bincike, rundunar ‘yan sandan Zamfara ta ce tana ƙoƙarin gano musabbabin tashin gobarar.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
UNICEF Ya Bukaci Hadin Kai Don Inganta Rayuwar Kananan Yara A Jigawa
Ofishin Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF da ke Kano, ya ce zai ci gaba da hada gwiwa da gwamnatin jihar Jigawa a bangarori da dama da suka hada da kiwon lafiya, da ilimi, da samar da abinci mai gina jiki, da kare yara, da al’umma.
Shugaban ofishin , Mista Rahama Rihood Farah ya bayyana hakan a Dutse, babban birnin jiharJigawa.
Ya kara da cewa, hadin gwiwar da UNICEF ya yi da gwamnatin jihar Jigawa ya samu nasarori da dama, kamar karfafa tsarin tantance yaran da suke cikin kangin talauci, ta hanyar binciken da aka gudanar a kwanan baya (GHS), da samar da muhimman tsare-tsare da tsare-tsare, da kuma sanya masu ruwa da tsaki a tsarin.
Ya bukaci shugabannin kananan hukumomin da su bayar da gudunmawarsu wajen bada gudunmawarsu domin magance halin kuncin rayuwa da kananan yara ke ciki a jihar Jigawa, ta hanyar amfani da kwararan hujjojin da za a yi amfani da su domin tsara bangarori daban-daban.
Ya ce binciken ya nuna cewa kashi 90 bisa 100 na yara a jihar Jigawa suna fama da matsanancin kangin talauci, yayin da kimanin kashi 86 bisa 100 ke fuskantar rashi a fannoni masu muhimmanci da suka hada da kiwon lafiya, da ilimi, da abinci mai gina jiki, da tsaftataccen ruwan sha, da sauransu.
Mista Farah ya bayyana bukatar hada hannu cikin gaggawa domin rage radadin talauci da inganta rayuwar yara a jihar Jigawa.
“Don karfafa kokarinmu na hadin gwiwa, muna neman goyon bayan gwamnati wajen samar da matakan da za su tabbatar da yin amfani da bayanan da aka samu na kananan hukumomi domin gudanar da abin da ya dace”.
“Sauran fannonin sun hada da amincewa da ƙayyadaddun manufofin kare lafiyar jama’a, da amincewa da daftarin dokar kare al’umma da aka yi wa kwaskwarima zuwa doka, da ƙara yawan kason kasafin kuɗi don shirye-shirye na musamman na yara, da tabbatar da yin rajistar haihuwa ga yara ‘yan ƙasa da shekaru biyar“, in ji Farah.
Usman Muhammad Zaria