Radio Nigeria Kaduna Sun Je Ta’aziyar Albabello
Published: 6th, February 2025 GMT
Mahukunta gidan Radiyon tarayya na kaduna sun kai wa iyalan Alhaji Bala Albabello ta”aziya wanda Allah ya yi wa rasuwa ranar litini 3 ga watan fabrairu na shekarar 2025.
Shugaban gidan Radion, Malam Buhari Awwalu ne ya jagoranci tawagar zuwa gidan marigayin dake Tudun Jukun a zaria.
Malam Buhari Awwalu ya jajantawa iyalan marigayin,inda ya yi addu’ar Allah ya bai iyalan hakurin rashin sa,kuma ya sa a rinka tunawa da kyawawan dabi’un sa na taimakawa marasa karfi da kuma Dora al’umma akan turbar kasuwanci.
Ya kuma roki Allah da ya sanya shi a aljannar firdausi.
Da ya ke jawabi a masadin iyalan,Alhaji Hassan Abdulwahab ya yi bayanin cewa marigayi Albabello ya sadaukar da rayuwar sa ce wajen hidimtawa al’umma.
Cikin mahukunta gidan Radion da suka rufa wa shugaban bayan sun hada mataimakin darakta mai kula da sashin mulki,Malam umar Alkali da mataimakin darakta mai kula da sashin shirye-shirye,Malam Idris Yahaya da mataimakin darakta mai kula da sashin talace-talace, Malam Musa Yahaya da mataimakin darakta mai kula da sashin cinikayya,Malam Abubakar Lawal Dutsen ma,da mataimakin darakta mai kula da wasanni da watsa shirye-shirye daga nesa,Malam Lawal Ali Garba da mai rikon shugaban sashin sabuwar hanyar yana labarai na zamani, Malam Umar usman Tsiga da shugaban sashin kula da na’urorin kwsmfuta,Malam Nasiru Umar chawai da mai binciken kudi,Malam Yusha’u Umar.
HALIRU HAMZA
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Ta aziya Zaria da mataimakin darakta mai kula da sashin
এছাড়াও পড়ুন:
Palasdinawa Ne Zasu Fayyanace Makomarsu Ba Wasu Dan Mulkin Mallaka Ba: Qalibof
Shugaban majalisar dokokin kasar Iran Muhammad Bakir Qalibof ya bayyana cewa falasdinawa masu kasa ne zasu fayyace makomar kasarsu, don haka shirin da wasu manya-manyan kasashen duniya suke dashi a kan makomar Falasdinu da Falasdinawa ba dai-dai bane kuma zamu yi yaki da shi.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Teran ta nakalto shugaban majalisar dokokin kasar Iran Mohammada Bakir Qolibft yana fadar haka a taron shuwagabannin majalisun dokoki na kasashen Asia a birnin Baku na kasar Azaibaijan.
Qolibof ya kuma kara da cewa shirin shugaban kasar Amurka yake yi na kwace gaza da kuma inda za’a maida Falasdinawa ba zai kai ga nasara ba.
Qalibof ya yi allawadai wadai da shugaba Trump kan shishigin da yake yi a cikin al-amuran Falasdinawa, da kuma yin watsi da kokarin Falasdinawa a gaza suke yi don kwato kasarsu.
Ya ce Iran ba za ta amince da duk wata kasa mai jin tana da karfi wacce za ta dorawa falasdinawa tunaninsa ba.
Shugaban majalisar ya bayyana cewa yakin da HKI ta fafata da falasdinawa a Gaza, da kuma kungiyar Hizbulla a kasar Lebanon, sun bayyana raunin HKI a fili, wannan duk tare da dukkan tallafin da take samu daga kasashen yamma musamman Amurka.
Daga karshe ya ce dole ne a sami yentacciyar kasar Palasdinu mai zaman kanta nan gaba.