Aminiya:
2025-04-14@18:10:16 GMT

Malamai sun fara yajin aiki a Ebonyi

Published: 6th, February 2025 GMT

Ƙungiyar Malamai ta Najeriya NUT reshen Jihar Ebonyi ta sanar da fara yajin aikin sai baba-ta-gani a ƙananan hukumomi bakwai na jihar sakamakon rashin biyan albashin watanni.

Yankunan da abin ya shafa sun haɗa da: Ebonyi, Edda, Ezza South, Ezza North, Ivo, Ishielu da Ƙaramar Hukumar Ohaukwu.

Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai Uwa ta fusata ta jefa ’yarta cikin kogi a Bayelsa

Ƙungiyar ta koka kan rashin biyan albashin sama da watanni uku ga malaman da ke Ƙananan hukumomin da abin ya shafa.

Hakan na ƙunshe ne a cikin wata sanarwa mai ɗauke da sa hannun sakataren ƙungiyar, Bassey Asuquo kuma aka rabawa manema labarai a Abakiliki babban birnin jihar a ranar Alhamis.

Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Bayan sanarwar da muka bayar a baya kan shirin fara yajin aikin, mun yi nazari sosai kan yadda shugabannin ƙananan hukumomi suka amince da biyan albashin mambobinmu.

“Ya zuwa ranar aiki ta Laraba, 5 ga Fabrairu, 2025, mun amince da cewa wasu ƙananan hukumomi sun biya albashin mambobinmu.

“Duk da haka, muna nadamar sanar da ku cewa shugabannin ƙananan hukumomi da dama sun gaza biyan kuɗaɗen albashin mambobinmu.

“A kan haka, an umurci dukkan mambobinmu na jihar da na reshen ƙananan hukumomin da abin ya shafa da su bi wannan umarni da kuma tabbatar da aiwatar da yajin aikin nan take daga ƙarfe 12:00 na daren ranar Alhamis 6 ga Fabrairu, 2025.

উৎস: Aminiya

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan

Hukumar kula da agaji ta MDD (OCHA) ta bada sanarwan cewa, gwamnatin HKI a yankin yamma da kogin Jordan ta kori Falasdinawa a gidaje 5 a yankin bayan sun rusa gidajensu. Hukumar ta kara da cewa wadanda HKI ta rusa gidajensu a yankin sun hada da yara 19 da da iyayensu 33 maza da mata 6.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto OCHA na cewa tun watan Maris da ya gabata zuwa yanzu, HKI ta rusa gidaje da gine-ginen Fafalsadinawa kimani 100 a yankin yamma da kogin Jordan wadanda suka hada da gabacin birnin Qudus da kuma sauran yankuna, da sunan an gina gidajen ba bisa ka’ida ba.

Banda haka suna kwace gonakin Falasdinawa don ginawa sabin yahudawan da suke shigowa kasar matsugunai.

Labarin y ace, a wasu lokutan yahudawan zasu tilastawa Falasdinawa rusa gidajensu da kansu ko kuma idan sun rusa su da kayan aikinsu su tilastawa Falasdinawan kbiyan kudaden aikin rusawan.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina
  • Boko Haram ta kashe mutum 300 ta kwace ƙananan hukumomi 3 a Borno — Ndume
  • Hukumar OCHA Ta Bayyana Cewa Yahudawan Sahyoniyya Sun Ninninka Ayyukan Korar Falasdinawa A Yamma Da Kogin Jordan
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • HKI Ta Jefa Boma-Bomai A Kan Asbiti Tilo Da Ya Rage Yake Aiki A Arewacin Gaza
  • Kallo Daya Mutum Za Yi Min Ya Gane Masana’antar Kannywood Ta Canza Rayuwata -Farida Abdullahi
  • Za A Samar Da Ababen Hawa Ga Malaman Sakandare A Jigawa
  •  Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • NIMASA Za Ta Adana Wa Nijeriya Dala Biliyan 400 A Shekara Daga Cazar Kudaden Safarar Kaya