HausaTv:
2025-04-14@18:17:14 GMT

Isra’ila Ta Umurci Sojoji Su Shirya Tsarin Fitar Da Faladinawa Dake So Daga Gaza

Published: 6th, February 2025 GMT

Ministan tsaron Isra’ila, Isra’ila Katz ya umarci sojojin gwamnatin kasar da su shirya wani shiri na “ficewar” Falasdinawa daga zirin Gaza.

Umarnin Katz ya biyo bayan shawarar Shugaba Donald Trump na tilastawa Falasdinawa Gaza barin zirin da kuma sanya Amurka ta mamaye yankin da yaki ya lalata.

“Na umurci IDF da su shirya wani shiri don ba da damar ficewa na radin kan mazauna Gaza,” in ji kakakin na Isra’ila a cikin wata sanarwa.

Katz ya bayyana cewa ya fadawa sojojin Isra’ila da su yi shirin da “zai ba da damar duk wani mazaunin Gaza da ke son barin yankin zuwa, ga duk wata kasa da yake son karba.”

Ministan tsaron Isra’ila ya kara da cewa “Tsarin zai hada da zabin fita ta kasa, da kuma shirye-shirye na musamman na jiragan sama da kuma na ruwa.”

Katz ya ce yana maraba da “tsarin da Trump ya dauka, wanda zai iya baiwa wani kaso mai yawa na al’ummar Gaza damar yin kaura zuwa wurare daban-daban na duniya.”

A wani labarin kuma kungiyar Hamas ta bukaci da a gudanar da taron gaggawa na kasashen Larabawa domin mayar da martani ga shawarar da shugaba Donald Trump ya gabatar na mamaye yankin Falasdinu da kuma korar al’ummar kasar.

 A cikin wata sanarwa da kakakin Hamas Hazem Qassem ya fitar, ya ce “Muna kira da a gudanar da taron gaggawa na kasashen Larabawa don tunkarar shirin korar Palasdinawa daga Gaza, inda ya bukaci kasashen Larabawa da su bijirewa matsin lambar Trump, su kuma jajirce,” yayin da ya yi kira ga kungiyoyin kasa da kasa da su dauki kwararan matakai kan shirin na Trump.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun Ceto Fasinjoji 16 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Filato

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hamas ta ce a shirye take ta sako dukkan fursunonin Isra’ila da suka rage, domin musanya fursunoni”
  • An Kaddamar Da Shirin Bidiyon “Bayanan Magabata Dake Jan Hankalin Xi Jinping” Na Harshen Vietnam
  • Sojoji Sun Ceto Fasinjoji 16 Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Filato
  • Jiragen Saman Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Luguden Wuta Kan Asibitin Baptist Da Ke Gaza
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • Gaza: Sojojin HKI Sun Sake Kai Wa Asibitin “Ma’amadani Hari
  • Sin Da Sifaniya Sun Daga Matsayin Hadin Gwiwa A Fannin Shirya Fina-finai
  • Sama da mutane 1,560 ne sukayi shahada tun bayan da Isra’ila ta koma kai farmaki Gaza
  • Isra’ila ta yi barazanar fadada hare-hare Gaza yayin da ta yanke Rafah daga birnin Khan Yunis
  • Ficewar Kasar Nijar Daga Rundunar Hadin Gwiwa Ta Kasa Da Kasa Barazana Ce Ga Tsaro -Hedikwatar Tsaro