Iran : ‘’Falasdinu Ta Al’ummar Falasdinu ce” Jagora
Published: 6th, February 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya bayyana cewa : Gabadayen Falastinu tun daga kogi har zuwa teku ta al’ummar Falasdinawa ce.
Jagoran ya jaddada goyon bayan Iran ne ga gwagwarmayar Falasdinawa kan kasarsu mai dimbin tarihi, tun daga kogin Jordan zuwa tekun Bahar Rum, kamar shafin offishin jagoran ya sanar.
Kallaman Jagoran na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban Amurka Donald Trump ya gabatar da wata shawara mai cike da cece-kuce na kaurar da Falasdinawa daga zirin Gaza da kuma sanya Amurka ta karbe yankin da yaki ya lalata.
Ta hanyar yada wannan sako a cikin harsuna da dama, Iran ta nanata kudurinta na tabbatar da Falasdinu.
Shugaba Trump na Amurka ya tsaya kai da fata cewa “kowa na kaunar” shirinsa na Amurka ta kwace zirin Gaza.
Ya fadi hakan duk da irin watsi da suka da bayyana shirin nasa da al’ummar Falasdinawa da shugabannin Gabas ta Tsakiya da gwamnatocin kasashen duniya suka yi.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Cibiya Mai Fafutukar Kare Hakkokin Falasdinawa “Global 195” Ta Shelanta Farautar Sojojin HKI Da Su KaTafka Laifukan Yaki
Cibiyar ta “ Global 196” ta bakin babban shugabanta ta sanar da cewa a cikin watanni 18 da su ka gabata, ta tattara bayanai akan laifukan yakin da Isra’ila ta tafka a Gaza.” Haka nan kuma cibiyar mai matsuguni a Birtaniya ta ce, ya zuwa yanzu ta tattara da dalilai da su ka dace da ka’idojin shari’a a kotunan manyan laifuka na kasar.
Har ila yau cibiyar ta ce, bayan kammala tattara bayanai a zango na farko, za kuma ta bude shafi na gaba domin kara samun wasu bayanan da za su tabbatar da cewa an yi wa Isra’ilawan hukunci a cikin kasashen duniya, musamman masu dauke da zama ‘yan kasashe biyu.
Wani shiri da wannan cibiyar take da shi,shi ne na samar da wasu cibiyoyin a cikin nahiyoyin duniya da samar da ka’idoji ta fuskar shari’a da su ka dace da na duniya da kuma na kasashe domin farautar wadanda su ka aikata laifukan yaki a Gaza, da fitar da sammacin kamo su, saboda su fuskanci shari’a.
Wadanda wannan cibiyar take son ganin sun fuskanci shiri’a, sun hada jami’an sojan HKI, da ‘yan siyasa da duk masu hannu a aikata laifukan yaki.
Ita wannan cibiyar ta kunshi kawance na lauyoyi daga kasashen Malysia, Turkiya, Norway, Canada, Bosnia, da kuma Birtaniya.
Ana kuma sa ran cewa anan gaba wasu lauyoyin daga wasu kasashen duniya za su shiga ciki,musamman a wannan lokacin da HKI ta bude wani sabon kisan kiyashin akan al’ummar Falasdinu.
Cibiyar ta kasa da kasa mai son ganin an yi wa Falasdinawa adalci, ta kuma hada da fitaccen lauyan nan dan kasar Afirka Ta Kudu John Dugard, da kokarin jawo lauyoyi daga dukkakin kasashen duniya.
Cibiyar za ta yi aiki domin ganin a kowace jaha da gunduma ta kasashen duniya an samar da hanyar hukunta wadanda su ka aikata laifukan yaki a Gaza.