Argentina Ta Sanar Da Ficewarta Daga Hukumar Lafiya Ta Duniya WHO
Published: 6th, February 2025 GMT
Gwamnatin kasar Argentina ta sanar da ficewarta daga hukumar lafiya ta duniya WHO.
Mai magana da yawun shugaban kasar Manuel Adorni ya fadawa taron manema labarai cewa, shugaban kasar Javier Milei, ya umarci ministan harkokin wajen kasar Gerardo Werthein, da ya dauki matakin janye Argentina daga hukumar lafiya ta duniya.
Adorni ya ce, ” ‘yan Argentina ba za su kyale wata kungiya ta kasa da kasa ta tsoma baki a harkokin da suka shafi ‘yancin kasarmu ba. “
Ya kara da cewa,”Ya kamata a fayyace cewa Argentina ba ta karbar kudade daga hukumar ta WHO don kula da lafiya, don haka, wannan matakin, kamar yadda wasu ke cewa, a kalla a shafukan sada zumunta, ba ya wakiltar asarar kudade ga kasar, kuma ba ya shafar ingancin ayyuka da hidimomi.”
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Hukumar EFCC Ta Kama Mutane 40 da Ake Zargi da Damfarar Intanet
Jami’an hukumar shiyyar Kaduna na hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, sun kama wasu mutane arba’in da ake zargi da damfarar yanar gizo a kananan hukumomin Bida da Minna na jihar Neja.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da shugaban hukumar EFCC, Dele Oyewale ya raba wa manema labarai a Minna babban birnin jihar Neja.
A cewarsa an kama su ne biyo bayan sahihan bayanan sirri da ke alakanta su da ayyukan damfara na intanet.
Kayayyakin da aka kwato daga hannunsu sun hada da motoci uku, na’urorin samar da wutar lantarki guda takwas, na’urar sanyaya daki samfurin Hisense guda daya, na’urorin sarrafa wutar lantarki guda biyu, babura 10, kwamfutocin tafi da gidanka guda takwas, na’urar magana ta bluetooth hudu da wayoyin android 60 da dai sauran kayyaki.
Za a gurfanar da wadanda ake zargin zuwa kotu da zarar an kammala bincike.
PR ALIYU LAWAL.