HausaTv:
2025-03-28@03:09:23 GMT

Argentina Ta Sanar Da Ficewarta Daga Hukumar Lafiya Ta Duniya WHO

Published: 6th, February 2025 GMT

Gwamnatin kasar Argentina ta sanar da ficewarta daga hukumar lafiya ta duniya WHO.

Mai magana da yawun shugaban kasar Manuel Adorni ya fadawa taron manema labarai cewa, shugaban kasar Javier Milei, ya umarci ministan harkokin wajen kasar Gerardo Werthein, da ya dauki matakin janye Argentina daga hukumar lafiya ta duniya.

Adorni ya ce, ” ‘yan Argentina ba za su kyale wata kungiya ta kasa da kasa ta tsoma baki a harkokin da suka shafi ‘yancin kasarmu ba. “

Ya kara da cewa,”Ya kamata a fayyace cewa Argentina ba ta karbar kudade daga hukumar ta WHO don kula da lafiya, don haka, wannan matakin, kamar yadda wasu ke cewa, a kalla a shafukan sada zumunta, ba ya wakiltar asarar kudade ga kasar, kuma ba ya shafar ingancin ayyuka da  hidimomi.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano za ta hukunta masu shigar banza a bikin Sallah

Gwamnatin Kano ta sha alwashin hukunta masu shigar banza ko cudanya maza da mata a lokacin bukukuwan Sallah Karama da za a yi.

Gwamnatin ta bayyana hakan ne ta bakin shugaban Hukumar Tace Fina-finai da Dab’i ta Kano, Abba Almustapha a wata sanarwa da ta fitar mai dauke da sa hannun kakakin hukumar Abdullahi Sani Sulaiman, inda ta ce matakin yunkuri ne na gwamnatin domin tsaftace yadda gidajen wasanni da kidan DJ ke shagalin bikin Sallah.

Ban sani ba ko zan tsaya takara a 2027 — Atiku Kwamishinan Abba ya yi murabus bayan watanni 7 da naɗinsa

“A kokarin ta na yaki da rashin da’a tare tsaftace yadda gidajen wasanni da masu kidan DJ za su gudanar da shagalin bikin sallah a Kano, Hukumar tace fina-finai da Dab’i karkashin jagorancin Abba El-mustapha ta bayyana shirinta na saka kafar wando daya da duk wani gidan wasa ko mai kidan DJ da aka samu da rashin da’a a yayin gudanar da bikin sallah a Jihar.

Hukumar ta shirya wata tawaga ta musamman da za ta kewaya gidajen wasannin a bikin sallah karkashin kulawar Alh. Abubakar Zakari Garun Babba Daraktan Dab’i na Hukumar, domin sanya ido da tabbatar ba a bai wa masu shigar banza ko shaye – shaye damar shiga gidajen wasannin ba.

“Haka kuma, hukumar ta hana hada maza da mata a guri daya a yayin bikin sallar. Tawagar za ta yi aiki ne dare da rana daga ranar daya ga sallah har zuwa lokacin da za’a kammala bikin sallar domin cimma nasarar aikin da ta sanya a gaba.”

El-mustapha ya kuma yi gargadi ga masu gidajen wasanni da masu sana’ar DJ, da su yi biyayya ga dokokin hukumar sau da kafa domin gujewa fushinta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Na Adawa Da Kara Yawan Kamfanoninta Cikin Jerin Wadanda Amurka Ta Takaita Fitar Da Kayayyakinsu
  • Nijar : An nada Janar Tiani, a mukamin shugaban rikon kwarya
  • Ahmad Lawan ya raba tallafin N27m da buhun shinkafa 300 a Yobe
  • Duniyarmu A Yau: Ranar Qudus Ta Duniya Ta Shekara 1446
  • Gwamnatin Kano za ta hukunta masu shigar banza a bikin Sallah
  • Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran
  • NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya
  • Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya
  • Ministan Lafiya Ya Yi Alƙawarin Inganta Tallafi Ga Likitoci A Hajjin 2025
  • Mutane Miliyan 9 Na Iya Kamuwa Da Cutar HIV Saboda Rashin Tallafi