Aminiya:
2025-04-15@00:49:44 GMT

Majalisa na son ƙirƙiro sabbin jihohi 31 a Najeriya

Published: 6th, February 2025 GMT

Kwamitin Sake Duba Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na Majalisar Wakilai, ya bayar da shawarar ƙirƙiro sabbin jihohi 31 domin ƙara yawan jihohin ƙasar nan daga 36 zuwa 67.

Shugaban kwamitin, wanda kuma shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Benjamin Okezie Kalu ne, ya bayyana hakan yayin zaman majalisar da ya jagoranta a ranar Alhamis.

Malamai sun fara yajin aiki a Ebonyi  Tinubu ya yi sauye-sauye a Jami’ar Abuja

Daga cikin sabbin jihohin da aka bayar da shawarar ƙirƙirar su, akwai Benue Ala, Okun, Okura, Confluence, Apa-Agba, Apa da Abuja, waɗanda za a samar daga jihohin Benuwe da Kogi, tare da babban Birnin Tarayya.

A Arewa Maso Gabas, an bayar da shawarar ƙirƙiro jihohin Amana daga Jihar Adamawa, Katagum daga Bauchi, Savannah daga Borno, da Muri daga Taraba.

A Arewa Maso Yamma, akwai jihohin New Kaduna da Gurara daga Kaduna, Tiga da Ghari daga Kano, da kuma Kainji daga Kebbi.

A Kudu Maso Gabas kuwa, akwai jihohin Etiti, Urashi, Orlu, Aba da Adada, waɗanda za su fito daga yankin gaba ɗaya.

A yankin Kudu Maso Kudu, ana son ƙirƙiro jihohin Ogoja daga Kuros Riba, Warri daga Delta, Bori daga Ribas, da Obolo daga Ribas da Akwa Ibom.

A Kudu Maso Yamma, an tsara sabbin jihohin Toru-Ebe daga Delta, Edo da Ondo, Ibadan daga Oyo, Lagoon daga Legas, Ijebu daga Ogun, Oke-Ogun daga Ogun, Oyo da Osun, da Ife-Ijesha daga Ogun, Oyo da Osun.

Idan wannan shawara ta samu amincewa, Najeriya za ta ƙara yawan jihohinta daga 36 zuwa 67.

Ana kyautata zaton lamarin zai kawo sauyi mafi girma a tsarin gudanarwar Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Ghari Majalisar Wakilan Najeriya Taraba

এছাড়াও পড়ুন:

Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa

Tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero da ke Kano (BUK) ya shirya wani taron bikin cika shekaru 50 da kafuwa tare da gudanar da taron kasa karo na uku.

Taron wanda aka yi wa take da “Ilimi Mai Sauya Rayuwa Don Gaba: Fuskantar Sabbin Kalubale da Buɗe Damar Samun Ci gaba” ya samu halartar manyan masu ruwa da tsaki daga sashen ilimi.

Da take jawabi a wajen taron, Minista a ma’aikatar Ilimi Farfesa Suwaiba Ahmed Sa’id ta bayyana cewa, a ƙoƙarin da gwamnatin shugaban ƙasa Bola Tinubu ke yi na ƙarfafa tsarin ilimi, ya amince da kashe Naira biliyan 120 don bunƙasa shirin fasaha da koyon sana’o’i (TVET) a Najeriya.

Ministar ta kuma bayyana cewa, gwamnatin tarayya ta amince da fitar da Naira biliyan 40 domin kammala aikin ɗakin karatu na ƙasa da aka yi watsi da shi, domin tallafawa bincike da cigaban karatu.

Farfesa Suwaiba ta ƙara da cewa, ma’aikatar ilimi ta tarayya ƙarƙashin jagorancin Minista Alausa ta ƙaddamar da Shirin Sabunta Hanyar Ilimi ta Najeriya (NESRI).

“Ina da burin mayar da Najeriya daga tattalin arzikin da ke dogara da albarkatu zuwa tattalin arzikin da ke dogara da ilimi, tare da rage yawan yara da ba sa zuwa makaranta, rage ƙarancin koyo, da samun  ƙara ƙwarewa.”

Yayin da yake buɗe taron, Shugaban Jami’ar Bayero Kano, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya bayyana nasarorin da sashen ya samu, inda ya ce ya samar da manyan mutane kamar ministocin ilimi biyu, shugabannin jami’o’i tara, da matan gwamnan jihar Kano guda uku, da sauran fitattun ’yan Najeriya da suka yi fice a fannoni daban-daban.

Yayin da yake yabawa taken taron da dacewarsa, Farfesa Sagir ya tabbatar da cewa jami’ar tana nan daram wajen tallafawa duk wani shiri da zai ɗaga matsayin ilimi zuwa na ƙasa da ƙasa.

A jawabinsa na maraba, Shugaban tsangayar Ilimi na Jami’ar Bayero Kano (BUK), Dakta Abubakar Ibrahim Hassan, ya jaddada yadda tsangayar ke  kokari wajen shirya harkokin ilimi da na kimiyya.

“Daga cikin nasarorin da Jami’ar BUK ta samu a kwanan nan akwai samun tallafin TETFUND guda biyu da kowanne ya haura naira biliyan 30, tare da lashe wani shirin koyar da harsuna biyu wanda Bankin Raya Musulunci da Hukumar Ilimin Firamare ta Kasa (UBEC) suka dauki nauyi.”

Taron ya yi armashi inda aka bayar da lambar yabo ga fitattun ‘yan Najeriya da suka hada da Shugaban Jam’iyyar APC na kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, da matarsa Farfesa Hafsat, da Minista a ma’aikatar Ilimi ta Jiha Farfesa Suwaiba, tsohuwar Ministar Ilimi Farfesa Rukayya, da Farfesa Isah Yahaya Bunkure da wasu da dama.

Daga Khadija Aliyu 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsangayar Ilimi Ta BUK Ta Yi Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafuwa
  • An rantsar da shugabannin ƙananan hukumomi 34 na Katsina
  • Abincin karnuka ya fi namu —Fursunonin Najeriya
  • NAJERIYA A YAU: Dalilan Farfaɗowar Boko Haram A Jihar Borno
  • Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci: Makiya Suna Hasadan Ci Gaban Kasar Iran
  • NATE Ta Rantsarda Sabbin Shugabanni Reshen Jihar Kaduna
  • A daina cutar ’yan Najeriya ta hanyar rabon kayan tallafi
  • ’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa
  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • MDD Ta Bukaci Taimako Dangane Rikicin Sudan Wanda Ya Isa Kasar Chadi