Aminiya:
2025-03-25@19:11:41 GMT

Majalisa na son ƙirƙiro sabbin jihohi 31 a Najeriya

Published: 6th, February 2025 GMT

Kwamitin Sake Duba Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na Majalisar Wakilai, ya bayar da shawarar ƙirƙiro sabbin jihohi 31 domin ƙara yawan jihohin ƙasar nan daga 36 zuwa 67.

Shugaban kwamitin, wanda kuma shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai, Hon. Benjamin Okezie Kalu ne, ya bayyana hakan yayin zaman majalisar da ya jagoranta a ranar Alhamis.

Malamai sun fara yajin aiki a Ebonyi  Tinubu ya yi sauye-sauye a Jami’ar Abuja

Daga cikin sabbin jihohin da aka bayar da shawarar ƙirƙirar su, akwai Benue Ala, Okun, Okura, Confluence, Apa-Agba, Apa da Abuja, waɗanda za a samar daga jihohin Benuwe da Kogi, tare da babban Birnin Tarayya.

A Arewa Maso Gabas, an bayar da shawarar ƙirƙiro jihohin Amana daga Jihar Adamawa, Katagum daga Bauchi, Savannah daga Borno, da Muri daga Taraba.

A Arewa Maso Yamma, akwai jihohin New Kaduna da Gurara daga Kaduna, Tiga da Ghari daga Kano, da kuma Kainji daga Kebbi.

A Kudu Maso Gabas kuwa, akwai jihohin Etiti, Urashi, Orlu, Aba da Adada, waɗanda za su fito daga yankin gaba ɗaya.

A yankin Kudu Maso Kudu, ana son ƙirƙiro jihohin Ogoja daga Kuros Riba, Warri daga Delta, Bori daga Ribas, da Obolo daga Ribas da Akwa Ibom.

A Kudu Maso Yamma, an tsara sabbin jihohin Toru-Ebe daga Delta, Edo da Ondo, Ibadan daga Oyo, Lagoon daga Legas, Ijebu daga Ogun, Oke-Ogun daga Ogun, Oyo da Osun, da Ife-Ijesha daga Ogun, Oyo da Osun.

Idan wannan shawara ta samu amincewa, Najeriya za ta ƙara yawan jihohinta daga 36 zuwa 67.

Ana kyautata zaton lamarin zai kawo sauyi mafi girma a tsarin gudanarwar Najeriya.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Adamawa Ghari Majalisar Wakilan Najeriya Taraba

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Siyo Man Jiragen Sama Fiye Da Ganga Miliyan 2 Daga Matatar Dangote

Amurka ta shigo da sama da ganga miliyan biyu na man jiragen sama daga matatar Dangote a watan Maris. Matatar ta tabbatar da hakan ne a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, inda ta ce hakan ya tabbatar da “nagartar da ba ta misaltuwa” na kayayyakin matatar da kuma aminci da kasashen duniya suka bai wa matatar. Nijeriyar Jiya Da Yau: Kiki-Kakar Sabgar ‘Yan Majalisu Alamar Deepseek” Ta Bude Kofar Gyara Na Kara Kunno Kai A Harkokin Duniya Duba daga  rahoton ma’aikatar sa ido kan zirga-zirgar jiragen ruwa ta Kpler, ta ce jiragen ruwa shida dauke da kusan ganga miliyan 1.7 na man jiragen sama daga matatar Dangote sun isa tashoshin jiragen ruwa na Amurka a wannan watan na Maris. Wani jirgin ruwa, Hafnia Andromeda, ana kyautata tsammanin zai isa tashar Everglades a ranar 29 ga Maris tare da kusan ganga 348,000 na man jirgin sama daga matatar Dangote.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Amurka Ta Siyo Man Jiragen Sama Fiye Da Ganga Miliyan 2 Daga Matatar Dangote
  • Gwamnatin Tarayyar Najeriya Ta Kafa Rundunar Daukin Gaggawa Don Magance Matsalolin Tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Ake Yi Wa ‘Yan Majalisar Ƙasa Kiranye
  • Ban bai wa majalisa haƙuri ba — Natasha
  • An yi wa Jakadan Afirka ta Kudu da Amurka ta kora tarbar Jamurumai bayan komawarsa gida
  • Ƴansandan Sun Gayyaci Sanata Karimi Kan Zargin Shigar Kungiyar Leƙen Asirin Rasha Majalisa’
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • Iran ta yi Allah-wadai da harin ta’addanci da aka kai a wani masallaci a kudu maso yammacin Nijar
  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu