HausaTv:
2025-02-22@06:31:45 GMT

Duk Wani Matsin Lamba Kan Iran Zai Cutura_ Araghchi

Published: 6th, February 2025 GMT

Gwamnatin Iran ta bayyana cewa duk wata matsin lamba kan kasar ta Donald Trump za ta cutura.

Iran dai ta caccaki matakin da shugaban AMurka ya dauka ind aya sanya hannu kan umurnin sanya sauraren matakn matsin lamba kan Tehran a game da shirinta na nukiliya.

Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana a wani sako a X cewa siyasar matsim lamba ta gaza a baya, kuma za ta ci karo da tsayin daka mai karfi.

Abbas Araghchi ya kara da cewa abu ne mai sauki a samu hanyoyin tabbatar da cewa Iran ba ta nemi kera makamin nukiliya ba.

To amma a sa’i daya kuma wajibi ne Amurka da kasashen yammacin duniya su dage takunkumin karya tattalin arziki da suka kakabawa Iran.

Dokar zartarwar da shugaba Trump ya rattabawa hannu na da nufin rage yawan man da Iran take fitarwa zuwa sifili da kuma kakaba ma ta takunkumi mai tsauri, da kuma dakarun kare juyin juya hali, da manyan sojojin kasar.

Har ila yau, ta shafi shirin nan na makamman ballistic na Tehran, da kungiyoyin dake goyan bayan ta a yankin kamar Hizbullah, Hamas da Houthis.

Kasashen Yamma suna zargin Tehran da hanzarta shirinta na nukiliya, musamman ta hanyar inganta sinadarin Uranium zuwa kashi 60 cikin 100, sabanin yarjejeniyar 2015 da manyan kasashen duniya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah

Tashar jiragen sama ta birnin Beirut tana cike da masu shiga kasar daga kasashen daban-daban don halattar jana’izar Shahidai kuma shuwagabannin kungiyar Hizbullah Sayyid Hassan Nasarallah da kuma Magajinsa Shahid Sayyid Hashimi Safiyyuddeen wanda za’a gudanar a ranar 23 ga watan Fabarairu da muke ciki.

Kamfanin tafiye-tafiye na “Ajuz Travillin Agency’ ya fadawa tashar talabijin ta Almanar kan cewa tun yawan jiragen sama masu zuwa daga kasashen waje suka nin nink tafiye-tafiyensu zuwa Beiru, daga cikinsu, akwai Iraq Air wanda yake zuwa Beiru  har sau biyu. Amma daga yau ya kara shi zuwa har sau ukku.

Kamama Egypt Air ya ninka zuwasa Beirut har sai yu. Da kuma Tarksih Air shi ya ninninka ta fiyasa zuwa kasar.

Labarin ya kara da cewa daga ranakun 20-22 ga watan Fabrairu ne ake saran samun masu zuwa Beirt mafi yawan don samun halattar jana’izar manya-manyan shidan.

HKI ce ta yi ruwan boma bomai kan sayyid Hassan nasaralla wanda ya kai ton 85 wanda ya kai shi ga shahada a shekarar da ta gabata, sannan kwanaki bayan haka ta kashe magajinsa Sayyid Safiyuddeen. A yakin watin 15 da kungiyar Hizbullah ta faffata da HKI.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kasar Sin Ta Bukaci G20 Ta Zama Karfin Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali A Duniya
  • Limamin  Juma’a Na Tehran Ya Jaddada Muhimmancin Hadin Kai A Tsakanin Al’ummar Musulmi
  • Tashar Jiragen Sama Ta Rafikul Hariri Int. Na Birnin Beirut Yana Ciki Da Masu Shiga Kasar Saboda Jana’izar Shaheed Nasarallah
  • INEC Ta Buƙaci Majalisa Ta kirkiro Dokar Hana ‘Yan Siyasa Zuwa Rumfunan Zabe Da Maƙudan Kuɗaɗe
  • NNPP ta rasa Ɗan Majalisa na farko da ya koma APC
  • Dangote Ya Koma Matsayi Na 86 A Jadawalin Masu Arziƙin Duniya
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Sarkin Qatar Ya Iso Tehran A Yau Laraba
  • Jagora Ya Gana Da Shuwagabannin Kungiyar Jihadul Islami A Nan Tehran