Duk Wani Matsin Lamba Kan Iran Zai Cutura_ Araghchi
Published: 6th, February 2025 GMT
Gwamnatin Iran ta bayyana cewa duk wata matsin lamba kan kasar ta Donald Trump za ta cutura.
Iran dai ta caccaki matakin da shugaban AMurka ya dauka ind aya sanya hannu kan umurnin sanya sauraren matakn matsin lamba kan Tehran a game da shirinta na nukiliya.
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana a wani sako a X cewa siyasar matsim lamba ta gaza a baya, kuma za ta ci karo da tsayin daka mai karfi.
Abbas Araghchi ya kara da cewa abu ne mai sauki a samu hanyoyin tabbatar da cewa Iran ba ta nemi kera makamin nukiliya ba.
To amma a sa’i daya kuma wajibi ne Amurka da kasashen yammacin duniya su dage takunkumin karya tattalin arziki da suka kakabawa Iran.
Dokar zartarwar da shugaba Trump ya rattabawa hannu na da nufin rage yawan man da Iran take fitarwa zuwa sifili da kuma kakaba ma ta takunkumi mai tsauri, da kuma dakarun kare juyin juya hali, da manyan sojojin kasar.
Har ila yau, ta shafi shirin nan na makamman ballistic na Tehran, da kungiyoyin dake goyan bayan ta a yankin kamar Hizbullah, Hamas da Houthis.
Kasashen Yamma suna zargin Tehran da hanzarta shirinta na nukiliya, musamman ta hanyar inganta sinadarin Uranium zuwa kashi 60 cikin 100, sabanin yarjejeniyar 2015 da manyan kasashen duniya.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi
Rundunar ’Yan Sandan Jihar Bauchi, ta kama wasu matasa huɗu da ake zargi da yin garkuwa da kuma kashe wani yaro ɗan shekara shida, Shuaibu Safiyanu, a ƙauyen Sade da ke Ƙaramar Hukumar Darazo.
Aminiya ta ruwaito cewar mahaifin yaron, Safiyanu Abdullahi ne, ya sanar da Sarkin garinsu, Musa Isah, cewa a ranar 20 ga watan Maris, 2025, ɗansa ya ɓace.
Ɗan sa-kai ya kashe matasa biyu a Borno Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na LallashiWashegari, wani ya kira shi a waya yana neman kuɗin fansa.
Da farko, ya nemi miliyan uku (₦3,000,000), amma daga baya suka rage zuwa Naira dubu ɗari biyu (₦200,000).
A ranar 21 ga watan Maris, aka gano gawar yaron a cikin daji, an ɗaure masa wuya da igiya.
Nan take aka kai shi asibiti, inda likitoci suka tabbatar da mutuwarsa.
Daga nan aka bai wa iyalansa gawarsa domin yi masa jana’iza.
Kakakin ’yan sandan Jihar, CSP Ahmed Mohammed Wakil, ya ce bayan samun rahoton lamarin, jami’an su suka fara bincike.
Sun fara binciken ne daga wajen POS da ke kusa da inda aka buƙaci a biya kuɗin fansar.
A yayin binciken, sun kama wani matashi mai shekara 23, Rabi’u Muhammadu daga ƙauyen Leka.
An gano cewa lambar wayarsa ce aka yi amfani da ita wajen kiran mahaifin yaron.
Sannan ’yan sanda sun gano asusun bankin da aka bayar don biyan kuɗin fansar: Lambar asusu: 0145285130 Sunan mai asusu: Ozochikelu Samson Banki: Union Bank PLC
Bayan kama Rabi’u, ya bayyana cewa Samson Ozochikel, mai shekara 35 daga ƙauyen Sade, shi ne ya shirya yadda za a sace yaron.
Ya kuma ambaci wasu matasa biyu, Muhammad Sani (Jingi), mai shekara 25, da Musa Usman (Kala), mai shekara 30, dukkaninsu daga ƙauyen Leka.
A halin yanzu, ’yan sanda suna tsare da su, kuma ana ci gaba da bincike a sashen binciken manyan laifuka (SCID).
Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, ya tabbatar da cewa za su tabbatar da an yi adalci.
Ya kuma roƙi jama’a da su ci gaba da bai wa ’yan sanda haɗin kai, tare da sanar da su duk wani abun zargi ta layin kiran wayar gaggawa 112 ko Police Control Room a lamba 08156814656.
Rundunar ta jaddada ƙudirinta na kare rayuka da dukiyar al’ummar jihar.