HausaTv:
2025-03-24@13:17:24 GMT

ICC Na Neman Shaidu Kan Ta’asar Da Aka Aikata A Gabashin DR Congo

Published: 6th, February 2025 GMT

Kotun hukunta manyan laifuka ta duniya na neman shaidu kan halin da ake ciki a gabashin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Congo.

Matakin zai shafi irin ta’asar da aka aikata daga ranar 1 ga watan Janairun 2022 zuwa yau, bisa la’akari da tashe-tashen hankula da aka yi a makonnin baya-bayan nan musamman a birnin Goma – babban birnin lardin Kivu ta Arewa.

Kotun ta ICC ta ce an jikkata dubban mutane tare da kashe daruruwan mutane a birnin Goma da kewaye.

Daga cikin wadanda harin ya rutsa da su har da fararen hula da dakarun wanzar da zaman lafiya, bayan shafe tsawon watanni ana gwabza fada tsakanin sojojin Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kwango da kungiyar M23 da kawayenta.

Ofishin mai gabatar da kara ya yi kira ga dukkan bangarorin da abin ya shafa, da shaidu, da kungiyoyin kasa da kasa, kungiyoyin farar hula, da su bayar da duk wata shaida da ke hannunsu, dangane da zargin laifukan da dukkan bangarorin suka aikata.

A nata bangaren, DRC tana shirin gabatar da kudiri ga kwamitin kare hakkin bil adama na Majalisar Dinkin Duniya a wannan Juma’a a birnin Geneva na kasar Switzerland, na neman a gudanar da bincike kan abin da ta kira “gaggarumin take hakkin dan Adam” a birnin Goma.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Wike Ya Kwace Filaye 4,794 A Abuja Saboda Rashin Biyan Kudin Ka’ida

“Saboda haka, za a soke sunayen kadarorin da suka shafe sama da shekara goma ba a biya musu haraji ba nan take, Bugu da kari kuma, ana bayar da wa’adin kwanaki 21 ga masu rike da gidajen da ake rike da bashin kudin haraji na tsawon shekara daya zuwa goma, sannan kuma za a soke sunayensu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Syria: SOHR ta fallasa jami’an tsaron sabuwar gwamnati na yi tsiraru kisan gilla
  • Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta
  • Hukumar Birnin Istambul Ta Dakatar Da Akram Imamoglu Daga Matsayinsa Na Magajin Garin Birnin
  • Dole Gwamnatin Tarayyar Nijeriya Ta Daina Barazana Ga Masu Sukar Ta – Amnesty
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  • Isra’ila : ‘Yan adawa sun kira zanga-zangar gama-gari bayan korar shugaban Shin Bet
  • Kwana Daya Bayan Kwace Fadar Shugaban Kasa, Sojojin Sudan Sun Kwace Babban Bankin Kasar
  • Wike Ya Kwace Filaye 4,794 A Abuja Saboda Rashin Biyan Kudin Ka’ida
  • Sojojin Sudan Sun Kwace Iko Da Fadar Shugaban Kasa A Birnin Khartum
  • An Yi Tarukan Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan More Damammakin Sin A Havana Da Doha