Aminiya:
2025-04-14@18:29:17 GMT

An ƙaddamar wa ’yan kasuwa sabon tsarin biyan haraji a Gombe

Published: 6th, February 2025 GMT

A ƙoƙarin bunƙasa tattalin arziƙin Jihar Gombe, Hukumar Tattara Kuɗaɗen Shiga ta jihar, ƙarƙashin jagorancin Hajiya Aisha Adamu, ta ƙaddamar wa ’yan kasuwa sabon tsarin biyan haraji.

An ƙaddamar da tsarin ne a sakatariyar Ƙungiyar ’Yan Kasuwa da ke cikin babbar kasuwar Gombe.

Majalisa na son ƙirƙiro sabbin jihohi 31 a Najeriya An tsinci gawar Ɗan Majalisar da aka yi garkuwa a jajibirin Kirsimeti

Hajiya Aisha ta jinjina wa haɗin kan ’yan kasuwa, musamman, Alhaji Sanusi Abdullahi Mai Rediyo.

Ta ce kuɗaɗen haraji suna da muhimmanci wajen aiwatar da ayyukan raya ƙasa don amfanin al’umma.

Ta yi kira ga ’yan kasuwa da su dage wajen biyan harajinsu na shekara-shekara, wanda kowane mai shago zai biya sau ɗaya kawai.

Hajiya Aisha ta kuma bayyana cewa an samar da hanyoyin biyan haraji masu sauƙi, ciki har da ofisoshin haraji, Intanet, da kuma hedikwatar Hukumar Tattara Kuɗaɗen Shiga.

Shugaban Ƙungiyar ’Yan Kasuwa, Alhaji Sanusi Mai Rediyo, ya tabbatar da cikakken goyon bayansu ga wannan tsari.

Shi ma Sakataren Tsare-tsare na ƙungiyar, Alhaji Sabo Coca Cola, ya jaddada muhimmancin haɗin kai domin cimma burin bunƙasa tattalin arziƙin jihar.

Sabon tsarin biyan harajin zai taimaka wajen ƙara kuɗaɗen shiga na cikin gida tare da inganta ayyukan ci gaba a Jihar Gombe.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: yan kasuwa gwamnati Haraji Sabon Tsari biyan haraji

এছাড়াও পড়ুন:

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esma’ila Bagaei ya godeawa ministan harkokin wajen kasar Omman kan yadda ya shirya ya kuma gabatar da tattaunawa tsakanin JMI da Amurka a birnin Mascat da kuma kai kawon da yayi a  tsakanin bangarorin biyu.

Kamfanin dillancin labaran IRNA na kasar Iran ya nakalto Bagaei yana bayyana haka a wani sakon da ya aika a cikin shafinsa na X  a jiya Asabar, ya kuma aika da sakon ne a dai dai lokacinda ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi yana kan hanyarsa ta dawowa Tehran, bayan tattaunawar. Ya kuma kara da cewa yana fatan Badr bin Hamad Al Busaidi zai ci gaba da wannan kokarin a ranar Asabar mai zuwa inda bangarorin biyu zasu sake haduwa, sannan har zuwa karshen tattaunawar. Bayan kammala tattaunawar dai,  shugaban tawagar JKI a tattaunawar kuma ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana a shafinsa na X kan cewa, tattaunawar ta yi armashi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mutum 45 Sun Rasa Rayukansu A Wani Sabon Hari A Filato 
  • ’Yan bindiga sun kashe mutane 40 a sabon hari a Filato
  • Salah Ya Kafa Tarihi Yayin Da Liverpool Ke Dab Da Lashe Gasar Firimiya
  • Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran ya godewa ministan harkokin wajen kasar Omman
  • Iran da Amurka zasu ci gaba da tattaunawa a mako mai zuwa
  • Axios: Makomar Tsarin Jarin Hujja A Duniya  Tana Girgiza
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Iyaye Mata Sun Bukaci A Rika Samar Da Kayayyakin Bada Tazarar Haihuwa Akan Lokaci
  • Mutane Da Yawa Sun Jikkata Bayan Fashewar Bam A Wata Kasuwa A Ikeja
  • NIMASA Za Ta Adana Wa Nijeriya Dala Biliyan 400 A Shekara Daga Cazar Kudaden Safarar Kaya