Hukumar Jin Dadin Alhazai ta jihar Jigawa ta ce ta mikawa hukumar alhazai ta kasa NAHCON kudaden aikin hajjin maniyyatan jihar  na shekarar 2025 kimanin naira biliyan 4.5.

Babban Daraktan hukumar Alhaji Ahmed Umar Labbo ne ya bayyana haka ga manema labarai a Dutse babban birnin jihar.

Ya ce hukumar ta aika wa NAHCON Naira Biliyan Huda da Miliyan Dari Biyar da Ashirin (4.

520), a yayin da take sa ran za ta kara biyan wasu kudaden kafin cikar wa’adin da NAHCON din ta bayar.

Ya bayyana cewa hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta baiwa jihar kujeru 1,809.

A cewarsa, tuni hukumar ta raba kashi 40 cikin 100 ga kananan hukumomin jihar domin gudanar da aikin hajjin bana.

Don haka Labbo ya bukaci Maniyyatan jihar da su gaggauta kammala biyan kudinsu kafin wa’adin da NAHCON ta bayyana, saboda rashin yin haka na iya sa su rasa kujerunsu.

Ya kuma bayyana cewa nan ba da dadewa ba hukumar za ta fara gudanar da taron bita ga maniyyata a cibiyoyin da wasu Malamai suka kebe domin alhazan jihar.

Yayin da yake tsokaci kan masaukin Alhazai, Labbo ya ce  hukumar ta samar da masauki na alfarma kusa da Masallacin Harami da ke birnin Makkah, domin alhazan jihar su sami damar gudanar da ayyukansu cikin sauki.

Don haka ya bukaci maniyyatan  da su ci gaba da bai wa hukumar hadin kai domin cimma burin da ake so.

Rediyon Najeriya ya ruwaito cewa, tun ffarko da hukumar ta sanar da sama da miliyan 8.4 a matsayin kudin aikin Hajjin shekarar 2025 ga maniyyatan jihar.

Shugaban hukumar ya bayyana cewar sun yi taro da jami’an hukumar na shiyoyi, wanda  aka gudanar a dakin taro na hukumar da ke Dutse.

Ya yaba da irin goyon baya da kuma kyakkyawar alakar aiki da ake samu a tsakanin mahukuntan hukumar da ko’odinetocin, inda ya yi addu’ar samun dauwamammen hadin gwiwa domin amfanin kowa da kowa da kuma ci gaban jihar.

Ya kuma  bayyana cewar sun yi taro da jami’an hukumar na shiyoyi, wanda  aka gudanar a dakin taro na hukumar da ke Dutse.

Usman Muhammad Zaria

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Hukumar Alhazai Jigawa

এছাড়াও পড়ুন:

Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99

Bubu da kari, abin mahimmancin shi ne, shi talakan Nijeriya zai iya gani a kas na irin wadannan shirye-shiyen da gwamnatin ke son aiwatarwa?

 

Fannin Da Gwamnatin Za Ta Zuba Kudaden:

A kasafin kudin na 2025, Gwamnatin Tarayya ta warewa bangaren tsaro Naira tiriliyan 6.11 wanda ya kai ta samar da karin kaso 88 daga cikin kasafin kudin da ta warewa fannin na Naira tiriliyan 3.25 a 2024.

Shin wannan burin na Gwamnatin zai iya cika, duba da yadda aka gaza dakile ta’addanci, ‘yan fashin daji, wanda idan ba a mayar da hankali ba, a 2025, tarihi ne zai sake mai-maita kansa.

An ware Naira tiriliyan 5.99 a cikin kasafin kudin don yin tituna, gadoji da kuma manyan ayyuka a babbar hanyar da ta tashi daga Legas zuwa Kalaba da ta Sokoto zuwa Badagry, inda aka samu karin da ya kai sama da kaso 350 sabanin Naira tirliyan 1.32 da aka ware a kasafin kudin bara.

Idan har da a gudanar da wadannan ayyukan, za su kara samar da ayyukan yi da habaka kasuwanci.

Bugu da kari, a kasafin kudin na 2025, an warewa ilimi, kiwon lafiya da bunkasa hazaka Naira biliyan 5.7 wanda ya kai kaso 161, sabanin Naira tiriliyan 2.18 da aka ware a kasafin kudi na 2024, inda fannin aikin noma ya samu Naira tiriliayan 3.73, wanda hakan ya nuna an samu kari mai yawa da ya zarta na Naira biliyan 362, inda an yin wannan karin ne, don a karya farashin kayan abinci a kasar.

 

Sai dai, shin ko wannan karin kudaden zai samar wa talakawan kasar sauki?

Amma wasu kwararu a Cibiyar Tsare-Tsare Da Bincike Kan Tattalin Arzikin Kasa (CEPR) ta yi nuni da cewa, idan har ba a wanzar da kuma kara kudi a cikin kasafin kudi hakan ba zai yi tasiri ba.

 

Kara Yawan Karbo Rancen Kudade:

Kudin ruwan da bashin da Gwamnatin ke biya ya lakume Naira tirilaya 16.3, wanda ya kai kaso 98, inda hakan ya nuna an samu karin Naira 8.25 a kasafin kudi na 2024.

Sai dai, wani babban kalubalen shi ne, yadda Nijeriya ke biyan bashin kudin ruwa na bashin da ta karbo fiye da wanda rake son kashewa a bangarorin ilimi, kiwon lafiya da samar da kayan aiki.

Gwamnatin ta yi hasahsne kudaden shiga da take son samu za su karu daga Naira tiriliyan18.32 zuwa Naira 36.35 trillion, wadanda suka kai karin kaso 123.19, musamman ta hayar tara haraji da zuba hannun jari na ketare.

Duba da yadda a arihin Nijeriya ka gaza tara kudaden shigar da ake sa ran tarawa, wasu kwararru a taron kungiyar tattalin arziki Nijeriya (NESG) sun yi garadin cewa, bai mai yuwa banen wadannan hasashen da aka yi su tabbata ba.

Kasafin kudin kasar ya rubanya a cikin shekara daya, amma duk da haka kudaden shigar kasar sun yi rauni.

Alal misali, a cikin kasafin kudin na 2025, ‘yan Majalisa sun samu karin Naira biliyan 344.85, wanda a kasafin kudi na 2024, suka samu karin Naira biliyan 197.93, inda kuma su ke son ‘yan kasar su kara jan damarar ci gaba da kula da rayuwarsu.

Bugu da kari, ‘yan Malasira Dokoki sun sun samawar da kansu karin sma da Naira biliyan 7 na kudaden sun a tafiye-tafiye, da kuma wasu dimbin kudaden da suka warewa kansu na jin dadi da na biyan kafafen ‘yada labarai.

A shirye-shiyen jin kan alumma, an ware Naira biliyan 723.68 kacal wanda aka kara kudin zuwa Naira biliyan 600, amma duk da haka, wani dan bangare kadan ne, aka kashe kan ayyukan gwamnatin.

Akwai dai dimbin buri da aka sanya a cikin kasafin kudin na 2025, wanda duk da wannan burin, cin abinci sauku a rana, na neman gagarar talakan kasar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gombe Za Ta Kashe Naira Biliyan 1.1 Don Samar Da Fitilun Hanya Masu Aiki Da Hasken Rana
  • Gwamnatin Jigawa Ta Nanata Dokar Haramta Kiwon Dare
  • Hikimar Gwamnatin Jihar Jigawa Na Kaddamar Da Shirin Gina Rijiyoyin Burtsatsan Noman Rani
  • Gwamnatin Jigawa ta ƙaddamar da shirin noman rani na Lallashi
  • Fashin Baki Kan Kasafin Kudin 2025 Na Naira Tiriliyan 54.99
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • Trump Ya Bayyana Dalilin Rufe Gidan Rediyon Muryar Amurka
  • Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai
  • Hajjin Bana: Maniyata 3, 155 Suka Yi Rijista a Kano
  • Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum