Gwamnan ya bayyana haka a yayin wata ziyarar ta’aziyya da ya kai yankin na Rimin Zakara a yammacin ranar Alhamis 06, ga watan Febarairun 2025.

 

A yayin ziyarar l, gwamnan ya yi alkawarin gina wa jama’ar yankin na Rimin Zakara katafaren Masallacin Juma’a a matsayin sadaka jariya ga wadanda suka rasu a dambarwar filayan yankin da Jami’ar Bayero.

Gwamnan ya yi kuma alkawarin samar da Asibitin sha-ka-tafi da samar musu da hanya da kai hasken wutar lantarki da rijiyoyin burtsatsai da bai wa iyalan mamatan jari da daukar dawainiyar karatun yaransu gwargwadon iko da kuma daukar nauyin jinyar wadanda suka ji rauni a yankin a yayin rusau da aka yi a makon da ya gabata.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari

Tsohon Mataimakin Shugaban Nijeriya kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a 2023, Alhaji Atiku Abubakar ya ziyarci tsohon shugaban Nijeriya Muhammadu Buhari a Kaduna.

Atiku ya samu rakiyar tsofaffin gwamnoni da suka haɗa da tsohon Gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai da tsohon Gwamnan Sokoto Aminu Waziri Tambuwal da wasu jiga-jigan ’yan siyasa.

An gano gawar makiyayi da ƙwato shanu a Filato Boko Haram: Zulum ya yi ganawar sirri da Shugabannin sojoji

Kamar yadda aka wallafa bidiyon ziyarar a Shafin Atiku na Facebook, an rubuta cewa sun ziyarci Buharin, kuma sun sha dariya.

“A matsayina na Wazirin Adamawa, na tsaya domin gudanar da shagungulan Sallah a Adamawa, inda na wakilci Sarkin Adamawa, Lamiɗo Fombina a wasu shagulgulan.

“Yau kuma na kai ziyarar gaisuwar Sallah ga Muhammadu Buhari wanda ya shugabanci ƙasar a tsakanin 2015 zuwa 2023. Na ji daɗin ziyarar, saboda kamar yadda ya saba, ya yi ta ba mu dariya sai da haƙarƙarina suka yi zafi.” Cewar Atiku.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zulum Ya Gana Da Yaron Da Aka Ci Zarafi, Ya Ba Shi Gida, Tallafin Karatu
  • An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo
  • ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara
  • Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • Ziyarar da Atiku ya kai wa Buhari ba ta dami APC ba —Ganduje
  • Yemen Ta Maida Martani Kan Wasu Cibiyoyin Ajiyar Makamai A Yaffa Don Tallafawa Gaza
  • Abubuwa Da Yawa Na Faruwa Ba Tare Da Sanin Tinubu Ba – Tsohon Ma’aikacin Aso Rock
  • Kashe-kashen Filato: Jami’an tsaro na sassauta wa masu laifi —Tsohon gwamnan soji
  • Atiku ya jagoranci manyan ’yan siyasa sun ziyarci Buhari