Aminiya:
2025-04-13@11:06:06 GMT

NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa

Published: 7th, February 2025 GMT

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Shin mene ne dalilin faɗuwar farashin tumatir warwas a kasuwa?

Idan ba a manta ba, a watannin baya farashin tumatir ya yi tashin gwauron zabo wanda aka daɗe ba’a ga irinsa ba.
A wancan lokacin, sai da farashin ya kai ga iyalai da dama sun haƙura da shi sun koma sayen na gwangwani ko na leda.

NAJERIYA A YAU: Tasirin Yankan Angurya A Rayuwar Mata DAGA LARABA: Yadda Al’adun Aure A Ƙasar Hausa Suka Koma ‘Event Centre’

Wannan ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokacin zai yi nazari a kai.

Domin sauke shirin, latsa nan

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: farashi

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja

Ana fargabar matafiya da dama sun rasu bayan kifewar wani  kwalekwale ɗauke da ’yan kasuwa a yankin Kogin Neja.

Hatsarin kwalekwalen ya auku ne ƙauyen Sokun da ke yankin Ƙaramar Hukumar Lapai, a sakamakon iska mai ƙarfi da ta haddasa juyawar igiyar ruwan.

Shaidu sun ce hatsarin ya auku ne a yayin da kwalekwalen ke ɗauke da fasinjoji da kuma buhunan shinkafa kimanin 200 daga ƙauyen Bugge na Jihar Kogi a zuwa ƙauyen Sokun na Jihar Neja a ranar Laraba da dare.

Wani mazaunin yankin, Baba Alhassan, ya shaida wa wakilinmu cewa, ba a kai ga tantance ainihin yawan fasinjojin da ke cikin kwalwkwalen a lokacin da lamarin ya faru ba, amma an yi asarar duk buhunan shinkafar a hastarin.

NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya

Ya bayyana cewa daga cikin mamatan har da wani mai sana’ar POS da ƙaninsa ’yan asalin ƙauyen Alaba da ke Ƙaramar Hukumar Lapai

Daraktan Hukumar ba da Agajin Gaggawa na Jihar Neja (NSEMA), Abdullahi Baba Arah, ya tabbatar da aukuwar lamarin, yana mai cewa ana ci gaba da aikin ceto da ƙoƙarin gano ainihin musabbabin hatsarin da kuma irin asarar da ta haifar.

Mazauna yankin sun bayyana cewa, “Sufurin ruwa shi ne kaɗai hanyar da ta rage da muke amfani da ita domin kai kayanmu kasuwanni saboda hanyar ta yi mummunan lalacewa.”

Wata ’yar kasuwa a yankin mai suna Fatima Muhammad, ta bayyana cewa, saboda nisan tafiyar, fasinjoji sukan yi tafiyar dare domin su isa kasuwa washegari da safe.

Fatima ta ce, “Babban ƙalubalen da muke fuskanta shi ne sufuri. Da kwalekwale muka dogara wajen kai kayanmu kasuwa. Wani lokaci kwalekwalen na ɗaukar lodi fiye da kima. Sai ka ga kwalekwale mai ƙarfin ɗaukar mutane 100 ya kwashi sama da haka. Amma ban ga laifin fasinjojin ba, musamman masu son su isa da wuri.”

Jama’ar yankin sun yi kira ga Gwamnatin Jihar Neja da ta Tarayya da su samar da wadatattun rigunan kariya da jiragen ruwa na zamani sannan su aiwatar da tsauraran hukunci kan masu karya doka.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • Yaya ‘Yan Siyasar Amurka Ke Kasafta Harajin Ramuwar Gayya?
  • Najeriya Tana Fatan Samun Dalar Amurka Biliyan $200 A Ayyukan Sararin Samaniya
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing
  • ’Yan kasuwa da dama sun mutu bayan kifewar kwalekwale a Kogin Neja
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
  • Matatar Ɗangote ta rage farashin fetur zuwa N865
  • Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur