Gwamnatin kasar Afirka ta kudu ta ki bada kai ga bukatun Amurka duk tare da barazanar sakataren harkokin wajen kasar Marco Rubio na fasa zuwa taron G20 a kasar

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Ronald Lamola ministan harkokin wajen kasar Afirka ta kudu na cewa

“kasarmu yentacciyar kasa ce, kan tsarin democradiya, sannan tana mutunta bil’adama, tana daidaito tsakanin kasa, babu bambamcin launin fata”

Lamola ya kara da cewa kasarsa na da tsarin zamanta kewa mai cikekken yanci daga duk wata kasa a duniya.

Ministan  ya kara da cewa, ba sauyin yanayi ne kawai muke tattaunawa a taron G20 ba,

Kafin haka sakataren harkokin wajen Amurka yace, shi ba zai halacci taro inda babu ambaton bukatun Amurka ba.

A ranakun 20-21 na watan Fabrayrun da muke ciki ne za’a gudanar da taron G20 a birnin Jorhamsboug na kasar Afirka ta kudu.

Amma Amurka tana korafin yadda Afrika ta kudu tasa HKI a gaba, kan kisan kiyashin Gaza da kuma wata dakar wacce shugaban kasar Cyril Ramaposa ya sanyawa hannu dangane da rabon filaye cikin adalci a kasar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Putin Ya Aike Wa Ayatullah Khamenei Da Murnar Idin Nowruz

Shugaban kasar Rasha Vladmir Putin ya mika sakon gaisuwar idin Nowruz na sabuwar shekarar hijira Shamsiyya ga jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei a daidai lokacin da ake gudanar da bukukuwan Nowruz, na  shigowar bazara da kuma sabuwar shekara ta Farisa.

Putin ya kuma aike da sakon fatan alheri ga shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian, kamar yadda fadar Kremlin ta sanar a ranar Juma’a.

Nowruz, wanda ke nufin Sabuwar Rana, ita ce ranar farko ta watan Farvardin na kalandar Farisa. Ranar  a mafi yawan lokuta tana kamawa ne a ranar 20 ga Maris amma a duk bayan shekaru tana tana kamawa  daidai da 21 ga Maris.

Majalisar Dinkin Duniya ta amince da ranar Nowruz ta duniya a shekara ta 2010, inda ta bayyana ta a matsayin bikin bazara na kalandar Farisa, wanda aka shafe shekaru sama da 3,000 ana gudanar da ita.

Hakanan a cikin shekarar 2009, an sanya Nowruz a hukumance a cikin jerin abubuwa na tarihi da al’adu na bil adama na hukumar UNESCO.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wang Yi: Kasar Sin Na Da Kwarin Gwiwa Kan Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Japan Da Koriya Ta Kudu  
  • Fadin Yankin Da Ke Fama Da Zaizayar Kasa Na Kasar Sin Ya Ragu A 2024 
  • Ranar Mata Ta Duniya: NPA Ta Mayar Da Hankali Wajen Kare ‘Yancin Mata –Dantsoho
  • Putin Ya Aike Wa Ayatullah Khamenei Da Murnar Idin Nowruz
  • Najeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Zargin Kisan Kiristoci A Kasar
  • An Yi Tarukan Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan More Damammakin Sin A Havana Da Doha
  • IAR da NAERLS Sun Shirya Taron Tattaunawa Da Masu Ruwa Da Tsaki Kan Noma Dawa A Najeriya
  • Zargin Kisan Kiristoci A Nijeriya: Fadar Shugaban Kasa Ta Yi Watsi Da Rahoton Amurka
  • ’Yan adawa sun shirya ƙalubalantar Tinubu a zaɓen 2027 – Atiku
  • Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe