Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya rattaba hannu a kan doka wacce ta yi allawadai da kutun kasa da kasa ta ICC saboda laifin fidda sammacin kama abokiyar Amurka firai ministan HKI da ta yi, sanadiyyar kissan kiyashin da ya yi a gaza.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Trump ya na fadar haka a lokacinda yake rattaba hannu a kan dokar tasa a jiya Alhamis.

Ya kuma kara da cewa kotun da ke birnin huqae ta wuce huruminta a lokacinda ta cutar kawar Amurka HKI tare da fidda sammacin kama shi.

A ranar tarlatan da ta gabata ce Benyamin Natanyahu ya tattauna da shugaban Trump wanda yayi masa alkawula da dama, daga cikin har da  kwace Gaza daga hannun Falasdinawa ya maida su kasar Masar ko kuma wani wuri. Sannan gyra Gaza ya mikashi  ga falasdinawa..

Dokar ta zargi kotun ICC da shiga cikin abinda bai shafeta ba, na kokarin gano take hakkin bil’adamann da Amurka ta yi a Afganistan ko kuma kisan kare dangin da HKI ta yi a Gaza.

Don haka shugaban ya dorawa jami’an hukumar ta ICC takunkuman tafiya zuwa Amurka, wanda ya hada da iyalansu da kuma duk wanda ya taimaka wajen fidda sammashin.

A cikin watan Nuwamban shekara ta 2024 ne kotun ta fidda sammacin kama Natanyahu da Glant saboda laifukan yakin da suka aikata a gaza.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu

Shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran ya ce kasashen wamma suna son kebe kansu da fasahar nukliya a tsakaninsu.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Muhammad Eslamu shugaban hukumar AEOI yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kafa a kasar Iran kuma ba wanda ya isa ya kauda shi. Sabanin abinda kasashen yamma suke so na hana sauran kasashen duniya mallaka fasahar nukliya, da kuma dogara da su kadai, su bada abinda suka ga dama ko  su hana gaba daya.

Ya ce JMI ta wuce wasu kasashen yamma a ayyuka da kuma sani da sarrafa makamashin Uranium, wanda ya tada hankalin wadannan kasashe, kuma suke sun han awasu kasashen duniya bin sawun kasar Iran na zama yentattu a wannan fage.

Islami ya kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kai wani matsayinda yana taiamakawa sauran kamfanoni na cikin gida ba tare da bukatar dogaro da kwararru ko kuma taimakon kasashen waje ba. Ya ce a halin yanzu iran na samar da wutan lantarki mai karfin magewats 20,000 tare da Makamashin Nukliya.

     

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa
  • Shugaban Kasar Iran Ya Mika Ta’aziyyar Ta Rasuwar Wanda Ya Assasa Hukumar  Makamashin Nukiliya Ta Iran
  • A Kasar Gabon Brice Oligui Nguema Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa
  • ‘Yansanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin Ɓarayin Wayar Wutar Lantarki Ne A Yobe
  • Brice Ologui Ya Lashe Zaben Shugaban Kasar Gaban Da Kashi 90.35% A Jiya Lahadi
  • Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
  • Dagewa Iran Takunkuman Zalunci Na Daga Cikin Manufofin Tattaunawa Da Amurka: Aref
  •  Limamin Tehran: Iran Ba Ta Tsoron Tattaunawa
  • NDLEA Ta Kama Wani Mutum Mai Shekaru 75 Da Laifin Safarar Muggan Kwayoyi
  • Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu