Shugaban Kasar Amurka Ya Sanya Hannu A Dokar Yin Tir Ta Kotun ICC Saboda Sammacin Kama Natanyahu Da Tayi
Published: 7th, February 2025 GMT
Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya rattaba hannu a kan doka wacce ta yi allawadai da kutun kasa da kasa ta ICC saboda laifin fidda sammacin kama abokiyar Amurka firai ministan HKI da ta yi, sanadiyyar kissan kiyashin da ya yi a gaza.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Trump ya na fadar haka a lokacinda yake rattaba hannu a kan dokar tasa a jiya Alhamis.
Ya kuma kara da cewa kotun da ke birnin huqae ta wuce huruminta a lokacinda ta cutar kawar Amurka HKI tare da fidda sammacin kama shi.
A ranar tarlatan da ta gabata ce Benyamin Natanyahu ya tattauna da shugaban Trump wanda yayi masa alkawula da dama, daga cikin har da kwace Gaza daga hannun Falasdinawa ya maida su kasar Masar ko kuma wani wuri. Sannan gyra Gaza ya mikashi ga falasdinawa..
Dokar ta zargi kotun ICC da shiga cikin abinda bai shafeta ba, na kokarin gano take hakkin bil’adamann da Amurka ta yi a Afganistan ko kuma kisan kare dangin da HKI ta yi a Gaza.
Don haka shugaban ya dorawa jami’an hukumar ta ICC takunkuman tafiya zuwa Amurka, wanda ya hada da iyalansu da kuma duk wanda ya taimaka wajen fidda sammashin.
A cikin watan Nuwamban shekara ta 2024 ne kotun ta fidda sammacin kama Natanyahu da Glant saboda laifukan yakin da suka aikata a gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Shugaban Hukumar Makamashin Nukliya Ta Kasar Iran Ya Ce Dukka Ayyukan Makamashin Nukliya A Cikin Gida Suna Tafiya Da Karfinsu
Shugaban hukumar makamashin nukliya na kasar Iran ya ce kasashen wamma suna son kebe kansu da fasahar nukliya a tsakaninsu.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Muhammad Eslamu shugaban hukumar AEOI yana fadar haka a jiya Jumma’a ya kuma kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kafa a kasar Iran kuma ba wanda ya isa ya kauda shi. Sabanin abinda kasashen yamma suke so na hana sauran kasashen duniya mallaka fasahar nukliya, da kuma dogara da su kadai, su bada abinda suka ga dama ko su hana gaba daya.
Ya ce JMI ta wuce wasu kasashen yamma a ayyuka da kuma sani da sarrafa makamashin Uranium, wanda ya tada hankalin wadannan kasashe, kuma suke sun han awasu kasashen duniya bin sawun kasar Iran na zama yentattu a wannan fage.
Islami ya kara da cewa kamfanin makamashin nukliya na kasar Iran ya kai wani matsayinda yana taiamakawa sauran kamfanoni na cikin gida ba tare da bukatar dogaro da kwararru ko kuma taimakon kasashen waje ba. Ya ce a halin yanzu iran na samar da wutan lantarki mai karfin magewats 20,000 tare da Makamashin Nukliya.