Leadership News Hausa:
2025-03-25@02:28:44 GMT

Wasu Ruwayoyi Game Da Yafiyar Manzon Allah (SAW)

Published: 7th, February 2025 GMT

Wasu Ruwayoyi Game Da Yafiyar Manzon Allah (SAW)

In an taba rarrauna a gabanka, kana da ikon kare masa, to ka kare masa, kin kare masa sakaci ne ba hakuri ba ne.

An ruwaito cewa, Annabi (SAW) bai taba dukan wata daga cikin Matansa ba ko kuma cikin masu masa hidima a gida ko a waje.

An kama wani Mutum da yake shirin kashe Annabi (SAW), aka gurfanar da shi gaban Annabi (SAW), sai jikinsa ya fara makyerkyata, Annabi (SAW) ya ce masa, kar ka firgita, ko da ka yi niyyar kashe ni, Allah ba zai dora ka a kaina ba.

Zaidu dan Sa’anatal Yahudi ya zo wurin Annabi (SAW) kafin ya Musulunta yana neman Annabi (SAW) ya biya shi bashin da ya karba a wurinshi. Sai ya fizgo rigar Annabi (SAW) daga kafadarsa, ya shake kwalar Annabi (SAW) sai ya ce “Ku ‘ya’yan Abdulmudallib taurin bashi ne gare ku,” sai Sayyadina Umar ya tamka masa da magana mai kaushi, shi kuma Annabi (SAW) yana ta Murmushi, Annabi (SAW) ya ce ya Umar “Da ni da mai amsar bashi, mun fi bukatar wani abu ba irin wannan yadda ka yi ba,” cewa za ka yi “Ya Muhammad, ka dinga kyakkyawan biyan bashi, shi kuma ka ce masa, ba a haka ya dace a dinga zuwa karbar biyan bashi ba,” sauran kwana uku lokacin biyan bashin ya yi. Sai Annabi (SAW) ya umarci Sayyadina Umar da ya biya masa bashin sannan kuma ya kara masa loka Ashirin na hatsin sabida tsorata shi da ya yi, sai wannan ya zama sanadin Musuluntar Bayahuden.

Yadda labarin yake shi ne, wannan Bayahude yana daga cikin manyan malaman Yahudawa, ya kasance yana cewa, tun da ya ga fuskar Annabi (SAW) ya ga alamun Annabtarsa duka sai guda biyu ne kadai bai jarraba ba, su ne: Hakurinsa yana riga fushinsa, tsananin wautar masu wauta ba ta fusata shi sai dai ta kara masa hakuri.

Sabida in tabbatar da wannan ya sa na je don in gwada shi, sai kuma na tabbatar da hakan kamar yadda Attaura ta fada. In ji Malamin Yahudawan (dan Sa’anata)

Hadisai da suke magana kan hakuri da afuwar Annabi (SAW) lokacin da yake da cikakken iko kan komai wurin zartar da hukunci, ya fi karfin a ce za a zo da su baki daya. Amma ya isa ma’auni a ce cikin Kabilar Kuraishawa ya taso kuma ya fara kira da a bi Ubangiji a cikinsu, wautar Jahiliyya a fili take a cikinsu har Allah ya taimake shi ya dora shi a kansu kuma ya hukunta shi a kansu.

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Kiyaye Ci Gaba Mai Dorewa A Huldar Sin Da Amurka Ya Dace Da Moriyar Sasssan Biyu

A yau Litinin ne kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin Guo Jiakun, ya jagoranci taron manema labarai na yau da kullum, inda wani dan jarida ya yi tambaya game da ko Sin za ta shiga tattaunawa da Amurka, game da hakan Guo Jiakun ya ce, a ko da yaushe kasar Sin na da imanin cewa, kiyaye zaman lafiya, da kwanciyar hankali, da ci gaba mai dorewa a dangantakar Sin da Amurka, ya dace da moriyar jama’ar kasashen biyu, da kuma fatan al’ummomin duniya baki daya.

Dangane da rikicin Ukraine kuwa, Guo Jiakun ya ce a baya-bayan nan, kungiyar “Kawancen zaman lafiya” kan rikicin Ukraine ta gudanar da wani taro a birnin New York, domin tattauna halin da ake ciki game da rikicin Ukraine, da kuma fatan samun dauwamammen zaman lafiya.

Ya ce kasar Sin za ta ci gaba da yin hadin gwiwa tare da kasashen duniya, wajen taka rawa mai ma’ana, don cimma nasarar warware rikicin Ukraine ta hanyar siyasa. (Safiyah Ma)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kiyaye Ci Gaba Mai Dorewa A Huldar Sin Da Amurka Ya Dace Da Moriyar Sasssan Biyu
  • Gwamna Uba Sani Ya Nada Sarkin Kauru Amirul Hajj Na Shekarar 2025
  • Ana ci gaba da gudanar da zanga-zangar goyon bayan Falastinu a kasashen duniya
  • NAJERIYA A YAU: Yadda watan Ramadana ke tasiri a harkokin kasuwanci
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [16]
  • Hanyoyi Goma Sha Daya Da Mace Za Ta Bi Domin Janyo Hankalin Mijinta
  • Mutumin da girgizar ƙasa ta razana ya shekara 2 yana zaune a cikin kogo
  • Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [15]
  • GMBNI Ta Yi Allah-wadai Da Kisan Gillar Wani Almajiri A Jihar Jigawa
  • An gudanar da gagarumar zanga-zangar nuna goyon bayan Falastinu a kasar Jordan