Kwamishiniyar Mata, Yara da Nakasassu ta Jihar Kano, Hajiya Amina Abdullahi, ta gargadi ma’aikatan Cibiyar Reformatory Institute ta Kiru da su guji karkatar da kayayyakin da aka ware domin gina cibiyar.

 

A yayin ziyarar duba aikin gyare-gyaren, kwamishina Amina ta jaddada muhimmancin yin amfani da kudaden da aka ware wajen abubuwa masu inganci a wannan cibiyar.

 

 

Cibiyar da aka sabunta za ta ƙunshi abubuwan more rayuwa na zamani, waɗanda suka haɗa da dakunan kwanan dalibai, asibiti, wurin shakatawa, wuraren aikin kafinta da walda, ɗakin cin abinci.

 

Kwamishina Amina ta yabawa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na inganta rayuwar al’ummar jihar Kano.

 

Ana sa ran kammala aikin gyaran nan ba da jimawa ba, daga nan ne za a bude cibiyar domin ci gaba da gudanar da ayyukanta.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gyara

এছাড়াও পড়ুন:

An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano

Jami’an tsaro sun kwace miyagun kwayoyi da kudinsu ya kai Naira miliyan 300 sannan ta kama mutane 650 da ake zargi a Jihar Kano.

Kwamitin Dawo da Zaman Lafiya da Kyautata Dabi’un Matasa ta Jihar Kano ce ta yi wanna kame a fadin jihar, kamar yadad ta bayyana a rahotonta.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Bakori, ya bayyana, ya bayana cewa mutum 150 daga ckin adadin an kama su ne kan laifukan dabanci da kwacen wayada da dangoginsu.

Kwamitin ya ce aikin haɗin gwiwar, ya yi wannan nasara ne bayan da suka kai samame a kan maboyar masu aikata laifuka da aka gano a kananan hukumomi takwas da ke garin Kano.

An sake kama wasu mafarauta ’yan Kano a Jihar Edo ’Yan bindiga sun kona masallacin Juma’a da asibiti da gidaje da Zamfara Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu

Hukumar ta bayyana cewa an gudanar da aikin ne tare da ’yan sanda da Hukumar Yaki da Miyagun Kwayoyi (NDLEA) da Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (NSCDC) da Hukumar Kula da Gidajen Yari da Hukumar Shige da Fice, da sauran hukumomi.

Da yake jawabi a wani taro da masu ruwa da tsaki a harkar tsaro, Shugaban Rundunar, Dakta Yusuf Ibrahim, ya ce ƙwace miyagun ƙwayoyin da aka kiyasta kimarsu a Naira miliyan 300 zai taka muhimmiyar rawa.

Ya kuma jaddada muhimmiyar rawar da tallafin al’umma ke takawa wajen dorewar ƙoƙarin Rundunar na inganta tsaron jama’a.

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Aminu Abdussalam, ya yaba wa nasarorin da Rundunar ta samu, yana mai tabbatar da kudurin gwamnatin jihar na magance ƙalubalen tsaro ta hanyar irin waɗannan matakai masu ƙarfi. Sa’annan ya jaddada buƙatar haɗin gwiwa tsakanin hukumomi da al’umma don samun ɗorewar tsaro.

Kwamishinan ‘Yan Sandan Jihar Kano,  ya yaba da ingancin ayyukan da aka gudanar bisa ga bayanan sirri, yana amai kira da a kafa wata kotu ta musamman domin hanzarta shari’ar waɗannan laifuka.

Kwamandan Hukumar NDLEA na Jihar, Abubakar Idris, ya yaba da haɗin gwiwar da ke tsakanin hukumomin tsaro kuma ya yi kira da a ci gaba da shidon magance matsalolin tsaro a Jihar Kano.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Namadi Ya Bada Ai hanyoyi 47 masu nisan kilomita 800 a sassan jihar.
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Tinubu ya kaddamar da aikin sake gyaran titin Abuja zuwa Kano
  • An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • Hajjin 2025: Shirye-shirye Sun Yi Nisa A Jihar Jigawa
  • Ukraine na Fuskantar Wata Barazana, Dangane Da Bukatar Amurka Na Kwace Iko Da Cibiyar Gas Na Rasha  A cikin Kasar
  • Sin Ta Mika Filayen Wasa Da Ta Yi Wa Gyaran Fuska Ga Senegal
  • An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato
  • An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
  • Dalilin Nijeriya Na Karbo Bashin Dala Biliyan 12 Daga Kasar Japan