Kwamishiniyar Mata, Yara da Nakasassu ta Jihar Kano, Hajiya Amina Abdullahi, ta gargadi ma’aikatan Cibiyar Reformatory Institute ta Kiru da su guji karkatar da kayayyakin da aka ware domin gina cibiyar.

 

A yayin ziyarar duba aikin gyare-gyaren, kwamishina Amina ta jaddada muhimmancin yin amfani da kudaden da aka ware wajen abubuwa masu inganci a wannan cibiyar.

 

 

Cibiyar da aka sabunta za ta ƙunshi abubuwan more rayuwa na zamani, waɗanda suka haɗa da dakunan kwanan dalibai, asibiti, wurin shakatawa, wuraren aikin kafinta da walda, ɗakin cin abinci.

 

Kwamishina Amina ta yabawa gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jajircewarsa na inganta rayuwar al’ummar jihar Kano.

 

Ana sa ran kammala aikin gyaran nan ba da jimawa ba, daga nan ne za a bude cibiyar domin ci gaba da gudanar da ayyukanta.

 

KHADIJAH ALIYU

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Gyara

এছাড়াও পড়ুন:

Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba

Shugaban kasar na Amurka Donald Trump ya wallafa wani sako a shafinsa na “Truth Social” da a ciki ya bayyana Volodymyr Zelenskyy dad an kama-karya, kuma abinda ya fi yi masa alheri shi ne ya yi wani abu da sauri, domin idan ba haka ba,zai yi asarar kasarsa baki daya.

Shugaban na kasar Amurka ya kara da cewa; Volodymyr Zelenskyy ya sa Amurka ta kashe dala biliyan 350 da ya shiga cikin yakin da ba zai iya samun nasara ba.

 Har ila yau, shugaban na Amurka ya ce, shi kanshi Volodymyr Zelenskyy ya yi furuci da cewa, rabin kudaden da mu ka aika masa sun bace, kuma ya ki gudanar da yin zabe, don haka masu goyon bayansa ‘yan kadan ne.”

Bugu da kari Trump ya ce, ko kadan bai kamata a ce yaki ya barke ba, domin yaki ne da babu yadda za a yi ya yi nasara ba tare da goyon bayan Amurka da kuma Trump ba, yana mai yin ishara da cewa, ahalin yanzu Amurka tana tattaunawa cikin nasara da Rasha domin kawo karshen yakin.”

Wani sashe na sakon Trump din ya kunshi cewa; Ina son kasar Ukiraniya, sai dai abinda Volodymyr Zelenskyy ya yi, ya munana, ya ruguza  kasarsa, kuma miliyoyin mutane sun mutu ba tare da dalili ba.

A gefe daya, kasashen turai sun mayar da martani akan maganganun na Trump, inda shugaban gwamantin Jamus ya ce shugaban kasar ta Ukiraniya ba dan dan kama-karya ba ne.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Ya Jinjinawa Jihar Jigawa
  • Shirin Rigakafin Cututtuka Na UNICEF/GAVI Ya Sami Cikakken Hadin Kan Gwamnatin Jihar Jigawa
  • An Bude Cibiyar Horar Da Malaman Harshen Sinanci A Ghana
  • Kasar Sin Ta Kammala Hako Rijiyar Fetur Mafi Zurfi A Yankin Asiya 
  • Kungiyoyin Falasdinawa A Gaza Sun Bukaci Yin Taron Musamman Domin Dakile Batun Tilasa Wa Mutanen Gaza Yin Hijira
  • Trump Na Amurka Ya Zargi Shugaban Kasar Ukiraniya Da Kama –Karya Da Kuma Rusa Kasarsa Ba Tare Da Wani Dalili Ba
  • Gidauniyar Tunawa Da Sir Ahmadu Bello Za Ta Gudanar Da Taronta Karo Na 11 A Bauchi.
  • UNICEF Ya Bukaci Hadin Kai Don Inganta Rayuwar Kananan Yara A Jigawa
  • ASUU Reshen Jami’ar KASU Ta Tsunduma Yajin Aikin Sai Baba-ta-gani
  • DAGA LARABA: Dalilan Da ’Yan Najeriya Ke Haɗa Buga-Buga Da Aikin Albashi