Kwara ta kammala horar da kwararrun ma’aikatan gona 1,000
Published: 7th, February 2025 GMT
Akalla manoma da ma’aikatan gona 1,000 ne gwamnatin jihar Kwara ta horas da su akan aikin gona da sarrafa ragowar amfanin gona don inganta amfanin gonakin da makiyaya ke amfani da su.
Da yake jawabi a karshen horon, a Ilorin, wanda Synergy Impact Limited ya shirya, tare da tallafin gwamnatin tarayya, bankin duniya da kuma shirin gwamnatin jihar Kwara akan kiyo da noma (L-PRES) kakakin majalisar dokokin jihar Kwara, Yakubu Danladi ya bayyana cewa shirin yana da karfin inganta ayyukan noma a jihar.
Kakakin majalisar wanda ya samu wakilcin shugaban kwamitin noma na majalisar, Issa Gideon, ya bayyana cewa shirin ya kara wa dimbin matasa kwarin gwiwa da jami’an noma da manoma wajen samar da kananan manaoma da sarrafa abincin dabbobi.
Ya godewa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu da gwamnatin jihar bisa bullo da shirin na L-PRES cewa aikin ya kara habaka noma a jihar.
Danladi, ya ce mahalarta taron, wadanda suka fito daga dukkan kananan hukumomin jihar 16, za su inganta harkar noma da kiwo a jihar da ma kasa baki daya.
Ya kuma bukaci mahalarta taron da su yi amfani da ilimin da aka samu a lokacin shirin, inda ya ce mutane na bukatar amfanin gona da kiwo a matsayin tushen arziki.
Dan majalisar ya ce samar da kananan dabbobin da matasa ke yi zai iya zama tushen gina tattalin arzikin kasar.
Ya kuma shawarci mahalarta taron da su kirkiro kayan aikin noma da injuna da aka samar musu a lokacin shirin horaswa a yankunansu daban-daban.
A nasa bangaren, shirin na jihar, Soji Oyawoye, ya bayyana fatansa cewa ilimi, kwarewa da kwarin gwiwa da mahalarta taron suka samu zai taimaka musu wajen aiwatar da ayyukan noma a yankunansu.
Ya kuma bukaci wadanda aka horas da su ma su horasda wasu akan wannan fasahar da suka samu ga manoma abokan aiki.
COV/ALI MUHAMMAD RABIU
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kwara mahalarta taron
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
Gwamnatin Amurka ta sanar da cewa: Ba ta neman tada tashin hankali tsakaninta da Iran
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Samuel Werberg ya bayyana cewa: Kasarsa ba ta neman kara ruruta wutar rikici da Iran, yana mai jaddada cewa har yanzu kofar diflomasiyya a bude take, duk kuwa da kakkausar murya da Amurka ta yi na kin amincewa Iran ta mallaki makamin nukiliya.
Werberg ya kara da cewa; Za su ci gaba da riko da siyasar matsin lamba da nufin dakatar da ci gaba a shirin nukiliyar Iran.
Kakakin na Amurka ya bayyana cewa, “Dole ne Iran ta nuna kyakkyawar niyyarta kafin ta yi magana kan duk wata nasara da za a samu.