A yau ne ake sa ran kwamitin kare haƙƙin dan adam na MDD zai yi zaman gaggawa kan yaƙin da ya rincabe a jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo.

Ƴan tawayen M23 da Rwanda ke mara wa baya dai sun karɓe iko da birnin GOMA.

MDD ta yi ƙiyasin cewa sama da farar hula 2,900 ne aka kashe, yayin da rahotanni ke cewa faɗa na kara yaɗuwa zuwa wasu sassan ƙasar, sannan take hakkin ɗan’adam na ƙara munana.

Jakadan Congo a Geneva ya ce gwamnatin ƙasar na buƙatar MDD ta gudanar da cikakken bincike kan hakan.

Kungiyoyin kare haƙƙin ɗan’adam sun yi amannar cewa ƴan tawayen M23 da sojojin Rwanda da na Congo duk sun aikata munanan laifuka.

Sai dai har yanzu Rwanda ba ta bayyana a hukumance cewa dakarunta na a cikin Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congon ba.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Yaki

এছাড়াও পড়ুন:

Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai

Majalisar wakilai ta tarayya ta yi watsi da zargin da ake yi ga ‘yan majalisar tarayya na cin hanci da rashawa domin marawa shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu baya na ayyana dokar ta baci a jihar Ribas.

Dan majalisa mai wakiltar mazabar Gwaram daga jihar Jigawa, Honarabul Yusuf Shittu Galambi, ne ya kare majalisar a yayin da ake ta cece-kuce kan batun kafa dokar ta-baci a jihar Ribas, inda wasu kungiyoyi ke zargin majalisar dokokin kasar da yin kasa a gwiwa wajen yanke hukunci.

Sai dai, Galambi a wata sanarwa da ya fitar a yau Asabar, ya ce babu gaskiya a ikirarin na cewa an tursasa ‘yan majalisar kan matakin da shugaban kasar ya dauka.

A cewarsa, yawancin mambobin sun goyi bayan matakin ne saboda ceto dimokuradiyya da kare muradun al’ummar jihar Ribas.

Dattawan Arewa sun buƙaci Tinubu ya dawo da Fubara kan kujerarsa

Mace ta farko ta zama shugabar ƙasar Namibia

Dan majalisar ya bayyana cewa majalisar ta yanke shawarar ne bisa son tabbatar da kishin kasa, hadin kan siyasa, zaman lafiya, da kare dimokuradiyya.

“Na yi mamakin yadda kafafen yada labarai suka rika yada labaran karya, musamman kan zargin da ake yi mana, cewa mun an tilasta mana mu zartar da kudurin goyon bayan matakin da shugaban kasa ya dauka a jihar Ribas da kuma karbar daloli”

“Ya kamata ‘yan Najeriya su yaba da rawar da ‘yan majalisar dokokin kasar ke takawa wajen neman shugaban kasa ya kafa wata tawagar sasanta yan siyasa kafin karewar wa’adin dokar ta-baci na watanni shida.

Ya kuma jaddada cewa dole ne a kare dimokradiyya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tunanin Raya Al’ummar Dan Adam Zai Tabbatar Da Makoma Mai Haske Ga Kowa
  • Wakilin Sin Ya Yi Bayani Game Da Tunanin Sin Kan Kare Hakkin Dan Adam Da Kin Amincewa Da Siyasantar Da Hakkin Dan Adam
  •  “Yan Ta’adda Sun Kai Hari Akan Masu Salla A Jamhuriyar Nijar
  • An ayyana zaman makoki na kwana uku bayan kashe mutum 44 a Nijar
  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • Ribas: Ba mu karɓi sisin kwabo domin amincewa da dokar ta baci ba – Majalisar Wakilai
  • Sin Ta Ba Da Jawabi A Kwamitin Kare Hakkin Bil’adama Na MDD A Madadin Kungiyar Abokantaka Ta Inganta Hakkin Bil’adama
  • Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri
  • Tinubu ya ba ni riƙon Ribas don wanzar da zaman lafiya — Ibas
  • Araghchi : Iran za ta mayar da amsa ga wasikar Trump cikin kwanaki masu zuwa