Sojojin Kenya 100 sun isa Haiti domin yaƙi da ƴandaba
Published: 7th, February 2025 GMT
Sama da sojojin Kenya 100 ne suka isa ƙasar Haiti, domin karfafa jami’an tsaron Haiti da kuma aikin dakarun wanzar da zaman lafiya na Majalisar Dinkin Duniya, a yaƙin da suke yi da gungun ƴandaba da suka addabi ƙasar.
Sai dai ana nuna damuwa kan yadda har yanzu dakarun suka gaza tabbatar da doka a babban birnin ƙasar, Porto Prince.
An yi ta raɗe-raɗin ayyukan dakarun sun zo ƙarshe, amma kwamandan rundunar, Godfrey Otunge ya ce lamarin ba haka yake ba.
Ya ce lokacin da yake magana da jakadun yana yi ne domin kawar da shakkun da ake yi na aikinsu, ya kuma shaida cewa ƙawancen na nan daram.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Kenya
এছাড়াও পড়ুন:
Badaƙalar Miyagun Ƙwayoyi: Kotun Amurka ta ba da umarnin fitar da bayanai kan binciken Tinubu
Wata kotu a Amurka ta umurci Hukumar Binciken Manyan Laifuka ta ƙasar (FBI) da ta fitar da bayanan sirri da aka samu kan Shugaba Bola Tinubu a lokacin wani binciken badaƙalar miyagun ƙwayoyi da gwamnatin ƙasar ta yi a shekarun 1990.
Jaridar Premium Times ta ruwaito Alƙalin kotun, Beryl Howell wanda ya ba da umarnin a ranar Talata, yana mai cewa babu ma’ana a rufe bayanan ba tare da an bayyana wa jama’a ba.
’Yan adawa sun zama kyanwar Lami duk da rinjayensu a Majalisa Amurka ta janye harajin kayan laturoni da ake shiga da su ƙasarA watan Yunin 2023 ce wani Ba’Amurke, Aaron Greenspan, a ƙarƙashin dokar ’yancin fitar da bayanai (FOAI) ya miƙa buƙatar a ofishin zartarwa na lauyoyin Amurka, da Hukumar FBI da Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun Ƙwayoyi (DEA) da kuma Hukumar Leƙen Asiri ta (CIA).
Wasu bayanai na cewa, a shekarar 1993 ce Tinubu ya sarayar da kimanin Dala 460,000 ga gwamnatin Amurka bayan mahukunta sun alaƙanta kuɗin da fataucin miyagun ƙwayoyi.
Ana iya tun cewa, wannan hujja ta rashin cancantar tsayawa takara manyan ’yan adawar Shugaba Tinubu — Atiku Abubakar da Peter Obi — suka gabatar a yayin ƙorafin zaɓen shugaban ƙasa na 2023.
Sai dai kotun sauraron ƙorafe-ƙorafen zaɓen ta yi watsi da ita tana mai tabbatar da nasarar Tinubu a babban zaɓen ƙasar ma 2023.