Martinez zai yi jinya har Karshen kaka
Published: 7th, February 2025 GMT
Ɗanbayan Manchester United Lisandro Martinez ba zai sake taka leda ba a sauran wasannin kakar nan saboda raunin da ya ji a guiwarsa, a ranar Lahadi.
An fitar da ɗanwasan ne mai shekara 27, a karawar da United ta yi rashin nasara a gida a hannun baƙinta Crystal Palace, raunin da tun a lokacin kociyan ƙungiyar Ruben Amorim ya bayyana a matsayin babbar matsala.
A ranar Alhamis ƙungiyar ta ce har yanzu ana duba yanayin raunin domin sanin yadda ya fi dacewa a yi masa magani da kuma tsawon lokacin da zai ɗauka yana jinya.
Sanarwar ta ce kowa a ƙungiyar yana yi wa Lisandro Martinez fatan warkewa sarai, kuma za su ci gaba da tallafa masa a kodayaushe.
Rashin Martinez babban ƙalubale ne ga Amorim wanda ke fama kan ganin ya dawo da ƙungiyar ta Old Trafford kan ganiyarta.
Yanzu United tana ta 13 a teburin Premier bayan kashin da ta sha a hannun Palace – rashin nasarar da shi ne na bakwai a wasa 13 na gida a bana.
A gobe Juma’a ne United za ta karɓi baƙuncin Leicester City, a karawar zagaye na huɗu ta cin kofin FA.
Martinez ya tafi jinyar ne yayin da United ɗin ke ɗari-ɗarin dawo na Luke Shaw, da ake ganin bai gama warkewa ba sarai, daga raunin da ya ji na ƙarshe.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Wasannni
এছাড়াও পড়ুন:
Falasdinawa 80,000 ne suka halarci sallar Juma’a a mako na uku na Ramadan a masallacin Al-Aqsa
An gudanar da Sallar Juma’a a mako na uku na watan Ramadan a Masallacin Al-Aqsa, duk kuwa da tsauraran takunkumin da gwamnatin yahudawan sahyoniya ta dauka, tare da halartar Palasdinawa 80,000.
Kamfanin dillancin labaran Al-Naba y bayar da rahoton cewa, dubun dubatar Falasdinawa ne suka gudanar da sallar Juma’a ta uku na watan Ramadan a masallacin Al-Aqsa, duk da matakai na kawo cikas da sojojin mamaya na Haramtacciyar Kasar Isra’ila suka dauka da kuma yanayin sanyi da ruwan sama a birnin Kudus.
Hukumar kula da lamurran addinin Musulunci a birnin Kudus ta bayar da bayanin cewa, masallata 80,000 ne suka gudanar da sallar Juma’a ta uku na watan Ramadan a masallacin Al-Aqsa.
Sheikh Khalid Abu Juma, limamin masallacin Al-Aqsa, ya ce a cikin hudubar sallar: “Watan Ramadan yana kawo azama da azama a cikinmu; Musulmai sun bar al’adun da suka saba a cikin saurin watanni; Suna nisantar da kansu daga al’adun da suka saba, tare da karfafa ayyukan tsarkeke ruhi da kusanci ga Allah.
Abu Juma ya jaddada cewa azumi yana karfafa nufi da kuma inganta azama, ya kara da cewa: Imani da azama suna da alaka da ruhi.
Ya ce: Yunkurin da makiya suke yi na rusa zaman lafiya da kwanciyar hankali ya sabawa koyarwar addinin muslunci da dukkanin addinai da aka saukar daga sama.
Sannan kuma ya yi ishara da abin da ke faruwa a Gaza, yana bayyana shi a matsayin aiwatar da wani mummunan kudiri na makiya a kan al’ummar musulmi na Gaza da ma Falastinu baki daya.