Aminiya:
2025-04-15@23:27:05 GMT

’Yan sanda sun sa dokar hana yawon dare a Gombe

Published: 7th, February 2025 GMT

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe ta haramta yawon dare, ta hanyar takaita zirga-zirga daga kare 12 na dare zuwa 5 na asubahi.

Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya sanar a ranar Alhamis cewa dokar za ta fara aiki ranar Juma’a, 7 ga Fabrairu, 2025.

Ya bayyana cewa an kafa dokar takaita zirga-zirgar ne bayan samun rahotannin barazanar tsaro.

Sanarwar ta ce, “takaita zirga-zirgar na da nasaba da karuwar barazanar tsaro da ke fuskantar al’ummar Gombe,” kuma a shirye rundunar take ta shawo kansu.

NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A Kasuwa Majalisa na son ƙirƙiro sabbin jihohi 31 a Najeriya Mutuwar Almajirai: Tinubu ya buƙaci a samar da matakan kare ɗalibai

DSP Buhari ya kara da cewa rundunar za ta kara ba da muhimmanci ga tsaron rayuka da dukiyoyin al’umma domin jihar Gombe ta kasance cikin aminci.

Ya bukaci jama’a su ba da hadin kai, yana mai kira ga iyaye da su gargadi ’ya’yansu su guji saba dokar domin duk mai kunnen kashin da aka kama zai yaba wa aya zaki.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran

Gwamnatin Amurka ta sanar da cewa: Ba ta neman tada tashin hankali tsakaninta da Iran

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Amurka Samuel Werberg ya bayyana cewa: Kasarsa ba ta neman kara ruruta wutar rikici da Iran, yana mai jaddada cewa har yanzu kofar diflomasiyya a bude take, duk kuwa da kakkausar murya da Amurka ta yi na kin amincewa Iran ta mallaki makamin nukiliya.

Werberg ya kara da cewa; Za su ci gaba da riko da siyasar matsin lamba da nufin dakatar da ci gaba a shirin nukiliyar Iran.

Kakakin na Amurka ya bayyana cewa, “Dole ne Iran ta nuna kyakkyawar niyyarta kafin ta yi magana kan duk wata nasara da za a samu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana barazanar korar sojojin Isra’ila da ke neman a kawo ƙarshen yaƙin Gaza
  • Gwamnatin Jigawa Ta Bukaci Jami’an Tsaro Mata Su Rika Sanya Hijabi Yayin Aiki
  • Xi Ya Isa Kuala Lumpur Domin Ziyarar Aiki A Malaysia
  • Tinubu Ya Kaddamar Da Ci Gaba Da Aikin Titin Abuja Zuwa Kaduna 
  • Rigima: Mawaƙi Portable ya kwana a hannun ’yan sanda
  • Iran Zata Yaye Labulen Ire-Iren Makamanta Na Musamman Da Ta Mallaka Domin Kare Kai
  • Gwamnatin Amurka Ta Yi Da’war Cewa; Ba Ta Neman Tashin Hankali Tsakaninta Da Iran
  • An kama kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • An kama miyagun kwayoyin N300m da mutane 650 a Kano
  • Bam Ya Halaka Mutum 8, Ya Jikkata Wasu Da Dama A Borno