Yadda bom din Boko Haram ya kashe mutane a hanyar kasuwa a Adamawa
Published: 7th, February 2025 GMT
Bama-bamai da mayakan Boko Haram suka binne sun kashe mutane biyu a hanyarsu ta zuwa kasuwa a Jihar Adamawa.
Kakakin ’yan sanda a jihar Borno, ASP Kenneth Daso, ya ce mutane shida ne a cikin motar a lokacin motar da ta taka bam din a ranar Talatar bayan ta taso daga Karamar Hukumar Hawul ta Borno zuwa Kasuwar Garkida ta jihar Adamawa.
“Ana zargin cewa ’yan Boko Haram ne suka dasa bama-baman, kuma motar da ke jigilar mutanen kauyen zuwa kasuwa a Garkida ta taka ta kuma ta fashe.
“Wani dan shekara 25 ya mutu nan take, amma sauran fasinjojin an garzaya da su asibiti domin yi musu magani,” inji shi.
Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki a Katsina NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A KasuwaYa ce ’yan sanda tare da sauran jami’an tsaro suna bakin kokarinsu wajen ganin sun kare yankin daga duk wata matsalar tsaro tare da yin kira ga jama’ar yankin da su kai rahoton duk wani abu da ake zargi.
Sai dai wani da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa wakilinmu cewa al’ummar kauyukan biyu na fuskantar hare-haren ta’addanci ta hanyar bama-bamai da aka dasa da daddare a kan hanyoyin karkara.
Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da su kara tura jami’ansu da makamai a yankin, domin hare-haren ta’addanci a Damboa da Chibok da kuma gefen dajin Sambisa na zama abin damuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa Boko Haram Garkida kasuwa Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Tinubu Ya Shirya Wa Kansa Mafitar Siyasa Kafin Zaben 2027
Ita maganar bada damar tsayawa takara ba tare da zaben fidda gwani ba an dauki matakin ne saboda yadda aka ga ‘yan adawa ko jam’iyyun adawa suke kokarin tayar da babbar kura mai hayaki,wa ita jam’iyyar mai rike da kambun mulki a 2027 domin “Ba a san maci Tuwo ba sai Miya ta kare”.
Ana dai ganin tarurrukan da aka yi na mambobin APC,wadanda suke ganin ba,a kyauta masu ba da kuma Shugabannin adawa suna yin wani shiri wanda zai iya sa wasu daga cikinsu su yi jerin Tururuwa na komawa jam’iyyar SDP,kamar dai yadda tsohon Gwamnan Jihar Kaduna,Malam Nasiru El Rufa’i ya fara kasancewa na farko wanda ake ganin akwai wadanda za su iya goyo masa baya.
Idan dai ba a manta ba mako biyu da ya wuce kwamitin zartarwar jami’iyyar ya nuna amincewa da ayyukan da Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi,hakan yana nuna ko dai su amince da bashi tikitin takara k kuma akashin hakan.
Akwai majiya mai tushe da ta bayyana a cikin taron kwamitin zartarwa na jam’iyyar da aka yi a Abuja ya nuna cewa kamar yadda abin yake an tattauna ne kan yadda tsarin Shugabancin jam’iyyar yake tun daga sama zuwa kasa,ko kuma daga na kasa, Jiha, Karamar Hukuma har zuwa na mazabar Kansila (Ward) an tattauna komai kan hakan.
Akwai majiyar da bata son a ambacin sunanta, da yi bayanin akwai wasu daga cikin Gwamnonin da basu amince da lamarin ba gaba daya ba,su ma da akwai wani tsarin da ake yi wanda zai basu damar su zabi wadanda suke son tsayawa takarar majalisar Jiha a Jihohinsu.
Idan har shi tsarin da aka yi an samu yin amfani da shi kwatin zartarwar jam’iyyar na kasa karkashin jagorancin Dakta Umar Abdullahi Ganduje da takwarorinsu na Jihohi za a barsu su ci gaba da tafiyar da jam’iyyar,saboda su taimakawa shirin da ake yi na kasancewar Bola Ahmed Tinubu shi ne dan takarar jam’iyyar.
Dankararar jam’iayyr daya tilo,suma ‘yan majalisun Dattawa da Wakilai wadanda suka ba jam’iayyar goyon baya tun daga lokacin da,Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya fara mulki.
“Shugabannin jam’iyyar sun san kura- kuren da aka yi a baya wanda matsala ce ta cikin gida wadda ta so sa wa jam’iyyar wani babban Tarnaki abinda daga karshe ya sa lakar jam’iyya ta kasance tamkar “Kazar da Kwai ya fashe ma ta a Ciki”. Wannan lokacin, ana bukatar ne kada a samu wata matsalar da zata iya kawo koma-baya. Hanya mafi dacewa ta yin hakan ita ce a ci gaba da tafiya irin yadda TSARIN Shugabancin jam’iyyar APC ya tsara ayi, domin a kaucewa aukuwar lamarin da zai sa ayi ta yin kumfar Baki saboda zaben fidda gwani.
“Idan za a tuna a zaben shekarar 2019, a babban zaben a Jihar Zamfara, mun rasa Jihar Zamfarar ne “inda jam’iyyar PDP ta samu dame a kala”,saboda rikicin cikin gida wanda ya fara ne sanadiyar zaben fidda gwani wanda aka ci gaba har zuwa 2023.
“Hakanan ma jam’iyyar APC, bata da ‘yan takara a Jihar Ribas saboda zaben fidda gwanin da mambobin jam’iyyar suka yi sau biyu kuma mabambanci.Hakanan ma akwai matsala wadda zaben Shugabannin jam’iyyar ya kusan gamawa da Jihar Imo. Idan ba lamarin kotu ba mun kusa rasa kujerar mu jam’iyyar PDP ta samu.”
Shugaban kasa ya samu rahoton sirri wanda ya nuna wadansu ‘yan jam’iyyar ba a kyautata masu ba, suna shirin barin jam’iyyar su koma wasu jam’iyyun adawa.
“Salon farko na su shi ne su samar da matsala cikin jam’iyyar APC idan an yi sabon zaben Shugabannin jam’iyyar.Domin maganin hakan, hanya mafita ita ce kada ayi zaben Shugabannin jam’iyyar,da kuma zaben kasa na jam’iyyar kafin babban zaben 2027.
“Hankalin sa kwance yake wajen tabbatar da babu wata matsala cikin jam’iyya,da kuma hana yiyuwar rigingimun bayan zabe wadanda suna iya kawo koma- baya. Ci gaba da wadannan Shugabannin ita ce mafita kuma zai taimaka wajen samun kwanciyar hankali kamar yadda majiyar ta ce”.
An samu labarin cewa jam’iyyar tana son ta amince da wata doka tunda har yanzu ba a bada sanarwa game da zaben kasa wanda za a ci gaba da tafiya da Shugabannin da ake da su a ci gaba da tafiya da su,tun daga na kasa har zuwa ta karshe ta matakin mazabar Kansila wato ward ke nan.
Matakin zai kara karfin Tinubu kan yadda taswirar jam’iyyar ta ke da kuma zabubbukan fidda gwani.
“Jam’iyyar ta shirya yadda zata zabi Shugabannin ta wanda a ranar ce, wani zai bada shawarar cewa a ci gaba da tafiya da Shugabnnin da ake fara tafiyar da su,tun daga na kasa har zuwa Ward har sai bayan babban zabe na shekarar 2027 kamar yadda bayanin ya nuna”.
Wadanda ake damawa da su a jam’iyya sun ce matakin shi ne abinda aka fi amincewa da shi, watao kwamitin zartarwar kasa na jam’iyyar ya amince da yadda Ganduje ya tafiyar da aikinsa tare da kwamitin gudanarwar sa.Matakin ya amince ne da yadda suka iya tafiyar da jam’iyyar duk kuwa da ta fuskanci matsaloli ma su yawa.Duk da hantarar da suka rika fama da ita sai da suka yi duk yadda suka iya suka samu aka amince da shi ne dantakarar ta na Shugaban kasa a shekarar 2027 ba tare da bata wani lokaci ba.
Hakanan ma ‘yan majalisun Dattawa dana Wakilai na jam’iyyar suma za su amfana da tsarin jam’iyyar su sake tsayawa ba tare da wata hamayya ba.
“Akwai maganar amincewa a jam’iyya kan lamarin amincewa da sa ita jam’iyyar ta sa kanta yin wani abinda zai iya kawo masu ko mata matsala. Yawancin ‘yan jam’iyyar da suke majalisun Dattawa da na Wakilai wadanda suka nunawa jam’iyyar ladabi da shi Shugaban kasa,ba sai sun tsaya sun fuskanci zabubbukan tantance gwani ba.Maimakon haka ma dama ce kawai za a basu su, su sake tsayawa takara ba tare da wata matsala ba sais u sake komawa kujerar tasu,”cewar wani babban kusa a jam’iyyar da baya son a ambaci sunansa.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp