Yadda bom din Boko Haram ya kashe mutane a hanyar kasuwa a Adamawa
Published: 7th, February 2025 GMT
Bama-bamai da mayakan Boko Haram suka binne sun kashe mutane biyu a hanyarsu ta zuwa kasuwa a Jihar Adamawa.
Kakakin ’yan sanda a jihar Borno, ASP Kenneth Daso, ya ce mutane shida ne a cikin motar a lokacin motar da ta taka bam din a ranar Talatar bayan ta taso daga Karamar Hukumar Hawul ta Borno zuwa Kasuwar Garkida ta jihar Adamawa.
“Ana zargin cewa ’yan Boko Haram ne suka dasa bama-baman, kuma motar da ke jigilar mutanen kauyen zuwa kasuwa a Garkida ta taka ta kuma ta fashe.
“Wani dan shekara 25 ya mutu nan take, amma sauran fasinjojin an garzaya da su asibiti domin yi musu magani,” inji shi.
Shugaban karamar hukuma ya biya wa al’ummarsa kudin wutar lantarki a Katsina NAJERIYA A YAU: Dalilin Faɗuwar Farashin Tumatur A KasuwaYa ce ’yan sanda tare da sauran jami’an tsaro suna bakin kokarinsu wajen ganin sun kare yankin daga duk wata matsalar tsaro tare da yin kira ga jama’ar yankin da su kai rahoton duk wani abu da ake zargi.
Sai dai wani da ya nemi a sakaya sunansa ya shaida wa wakilinmu cewa al’ummar kauyukan biyu na fuskantar hare-haren ta’addanci ta hanyar bama-bamai da aka dasa da daddare a kan hanyoyin karkara.
Ya kuma yi kira ga jami’an tsaro da su kara tura jami’ansu da makamai a yankin, domin hare-haren ta’addanci a Damboa da Chibok da kuma gefen dajin Sambisa na zama abin damuwa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Adamawa Boko Haram Garkida kasuwa Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Zargin Daukar Nauyin Boko Haram: Tinubu Na Ganawar Sirri Da Akpabio A Villa
Taron dai na zuwa ne sa’o’i kadan bayan da majalisar dattawan kasar a ranar Laraba ta gayyaci shugabannin hukumar leken asiri don gudanar da bincike kan zargin da dan majalisar dokokin Amurka, Perry Scott ya yi na cewa, hukumar bayar da tallafi ta kasa da kasa ta Amurka, USAID na tallafa wa kungiyoyin ta’addanci ciki har da Boko Haram.
Da yake jawabi a zaman taron na ranar Laraba, Akpabio ya ce Nijeriya ba za ta bar Hukumar USAID ta ci gaba da aiki a Nijeriya ba idan aka same ta da laifin daukar nauyin ta’addanci.
Ya ci gaba da cewa, yana da muhimmanci Nijeriya ta tabbatar da gaskiyar wannan zargi.