Leadership News Hausa:
2025-04-23@21:54:52 GMT

‘Yansanda Sun Kama Mutum Uku Da Kokon Kan Mutum A Imo

Published: 7th, February 2025 GMT

‘Yansanda Sun Kama Mutum Uku Da Kokon Kan Mutum A Imo

Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A ci gaba da kokarin da rundunar ‘yansandan Jihar Imo ke yi na dakile ayyukan ta’addanci a jihar, jami’an shalkwatar sashen Okigwe tare da hadin gwiwar mazauna unguwar Ogii a ranar 3/02/2025, sun kama wasu mutum uku da aka samu da kokon mutum, kaza da fararen kaya a kan titin Okigwe-Umuahia Edpressigwe.

“Mutum ukun da aka kama—Patrick Okoere, Ifeanyichukwu Anyaemeka, da Chukwuemeka Onyekachi 20—ana kan bincike a halin yanzu. Yayin da ake yi masa tambayoyi, Patrick ya bayyana cewa kawun nasa, Osunta Oko, ya nemi ya sayo kokon kan mutum. Ya yi ikirarin cewa ya same shi ne a bakin kogi a kan babbar hanyar Okigwe-Umuahia, yankin da rundunar ke samun labarin sace-sacen mutane.

“Rundunar ‘yansandan Jihar Imo na ci gaba da bin Osunta Oko da sauran masu hannu a cikin wannan lamari mai tayar da hankali. Bugu da kari, ana gudanar da bincike na DNA don sanin ainihin mai kokon.

“Kwamishanan ‘yansandan jihar, CP Aboki Danjuma, ya tabbatar wa jama’a cewa rundunar ‘yansandan ta jajirce wajen ganin ta kare lafiya da tsaron daukacin mazauna yankin. Ya kuma jaddada cewa za a yi adalci kuma wadanda ake zargin za su fuskanci hukunci bayan kammala bincike.”

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hisbah ta kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi

Hukumar Hisbah ta kama wata mata mai sana’ar ɗan wake kan zargin ta da yin lalata da wani almajiri dan shekara 14 a garin Azare da ke Jihar Bauchi.

Shugaban Hukumar ta Hisbah na shiyyar Katagum da ke Azare, Malam Ridwan Muhammad  Khairan ya bayyana cewar, ana zargin matar, wadda ake kira Baba Mai Ɗan Wake da laifin yin fasikanci ta hanyar tilasawa da yaudara da wani almajiri dan kimanin shekaru 14, bayan ta sanya masa maganin ƙarfin maza a cikin lemon kwalba don ya riƙa biya mata buƙata.

Ya ce almajirin ya haɗu da Nana Mai Ɗan Wake da yake mata wanke-wanke a Sabuwar Tashar Jama’are ne, a cikin garin Azare, inda ta buƙaci ya riƙa zuwa gidanta yana kwana, inda ta rika yaudarar sa har ta riƙa yin lalata da shi.

A cewar Malam Ridwan Mohammed Khairan, sun cafke matar ne bayan samun labari cin zarafin almajirin ta hanyar neman sa da ya riƙa biya mata buƙata irin ta mata da miji. Ya ce almajirin da kansa ya gudu ya nemi mai unguwa domin a kuɓutar da shi daga wannan hali da ta sanya shi ciki.

Don haka suka kai rahoton ga Hukumar Tsaron Farin Kaya Sibli Difens (NSCDC) aka kamo ta aka yi mata binciken kwakwaf, daga nan aka kai ta Bauchi ofishin masu binciken manyan laifika (CID) don kammala binciken kafin a mika ta ga kotu.

Wata majiya ta ce wajen da matar take sana’ar dan waken ya zama babban dandalin ɓarayi da ’yan shaye-shaye da ƙananan mata masu zaman kansu, domin duk wadda aka kama a samame, takan ce a wajen baba mai ɗan wake take.

Da aka tambayi almajirin abin da ke faruwa tsakaninsa da ita? Ya ce da farko bara yake zuwa, sai ta ce, ya rika zuwa gidanta tana ba shi abinci.

Ya ce da yake zuwa gidanta bayan ta tashi a kasuwancinta, sai ta riƙa kai shi ɗakinta tana ba shi abinci da lemon kwalbar da take sa maganin a ciki, tare da umartar sa ya riƙa matsa mata jikinta daga nan sai ta rika jan sa kanta tana kama gabansa tana sawa a cikin nata.

Yaron ya ce haka suka rika yi tun kafin azumi har bayan azumi, alhali shi ba abin da yake ji sai ciwon baya da yake addabar sa, wanda hakan ta sa ya gudu ya yi ƙara wajen mai unguwa.

Yanzu dai Shugaban Ƙungiyar Alarammomi na Ƙasar Katagum, Alaramma Husaini Gwani Gambo da Ƙungiyar Mata Musulmi ta FOMWAN da Ƙungiyar Matasa Masu Neman Hakkin Dan Adam, sun sa hannu don ganin an yi hukunci a kanta da bukatar tashinta a garin Azare.

Shugaban ƙungiyar alarammomin ya tabbatar da cewar, za su yi duk yadda za su yi don ganin an bi musu hakkin wannan cin zarafin da aka yiwa almajirinsu ba don ganin ya zama darasi ga wasu irin ta.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ƙasurgumin Ɗan Fashin Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Mutu Bayan Arangama Da ‘Yansanda A Kano
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana China Da Rasha A Matsayin Abokai Na Tushe Ga Iran
  • ’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi
  • Hanyoyin da za a magance rikicin Filato — Masana
  • Iran Ba Ta Da Niyyar Tattaunawa Da Amurka A Fili Bainar Jama’a Kan Shirinta Na Makamashin Nukiliya
  • Hisbah ta kama tsohuwa kan zargin lalata da almajiri a Bauchi
  • Miji ya yi wa matarsa saki 3 a ofishin ’yan sanda
  • Kakakin Ma’aikatar Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Babban Abin Da Suke Bukata Shi Ne Daga Takunkumi
  • Kungiyar Kare Hakkin Dan Adam Ta Amnesty International Ta Ce; Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ba Ta Dace Da Bincike Laifukan Sojojinta Ba
  • Ambaliya ta kashe mutum 3 ta lalata hekta 10,000 na shinkafa a Neja