Aminiya:
2025-03-26@11:44:23 GMT

Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi

Published: 7th, February 2025 GMT

Mayaƙan Lakurawa sun kashe farar hula ɗaya tare da jikkata wasu shida a yankin Gulma da ke Karamar Hukumar Argungua Jihar Kebbi.

Da misalin ƙarfe 11 na dare ne maharan suka suka wa yankin yayin da mazauna suke tsaka da barci a ranar Alhamis suna harbe harbe-harbe.

Shugaban Ƙaramar Hukumar Argungu, Aliyu Sani Gulma, ya bayyana cewa waɗanda maharan suka yi raunin harbi suna samun kulawa a Asibitin Tarayya da ke Birnin Kebbi, babban birnin jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Argungu Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran

Bayan gazawar tattaunawar da hukumar ta IAEA ta yi da Tehran, babban daraktan hukumar Rafael Grossi ya jaddada muhimmancin komawa kan teburin shawarwari nan gaba don tabbatar da cewa Iran ba ta mallaki makamin nukiliya ba.

Hukumar kula da makamashin nukiliya ta kasa da kasa ta ce tattaunawar da ta yi da wani babban jami’in kasar Iran a baya-bayan nan, ba a samu wani ci gaba kadan ba a cikin binciken nukiliyar da aka shafe shekaru ana yi kan kasar Iran, yana mai jaddada bukatar gaggauta warware takaddamar diflomasiyya da ke tsakanin Tehran da Washington.

A wata hira da Bloomberg babban darektan hukumar Rafael Grossi ya tabbatar da cewa nan ba da jimawa ba zai koma Tehran domin ci gaba da tattaunawa da jami’an Iran. “Muna kan wani muhimmin mataki,” in ji Grossi, yana mai cewa wadannan tattaunawa za su iya taka muhimmiyar rawa a nan gaba.

Grossi ya kara da cewa shugaban kasar Amurka Donald Trump ya aike da wasika zuwa ga jagoran ruhin Iran, wanda ke nuni da bukatar cimma fahimtar juna da ke musanta yuwuwar Iran ta mallaki makamin nukiliya.

A sa’i daya kuma, Grossi ya jaddada bukatar shugabannin kasashen duniya su yi taka-tsan-tsan da kamewa, a daidai lokacin da ake ci gaba da tafka mahawara ta kasa da kasa game da bukatar dakile makaman nukiliya.

A cikin jawabinsa, Grossi ya bayyana cewa, duniya na fuskantar kalubale guda biyu: a bangare guda, akwai batutuwan da ba a warware su daga baya ba, a daya bangaren kuma, damar da ta kunno kai na cimma wata yarjejeniya nan gaba da za ta kai ga cimma matsaya kan batun nukiliyar Iran na dogon lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar IAEA ta yi ishara da yiwuwar sake komawa teburin tattaunawa tare da Iran
  • Gobarar daji ta kashe mutum 24 a Koriya ta Kudu
  • NIDCOM: An Ceto ‘Yan Nijeriya Sama Da 950 Daga Gidajen Kurkuku A Libya
  • NUJ Ta Bada Tallafin Azumi Ga Iyalan Mambobinta Da Suka Rasu A Jihar Kebbi
  • Isra’ila ta kashe Falasdinawa 61 cikin sa’o’i 24
  • ‘Yansanda Sun Cafke Mutum 2 Kan Zargin Kashe Ɗan Achaɓa Da Sace Babur Ɗinsa A Bauchi 
  • Matasa Sun Daka Wawasu Kan Tirelar Kayan Agajin Ramadan Na Seyi Tinubu A Gombe 
  • Ɗansanda Ya Kashe Matar Abokin Aikinsa, Ya Jikata Wasu Biyu A Ribas
  • ’Yan bindiga sun kashe jami’an tsaro 10, sun jikkata 14 a Zamfara
  • Matasa sun kashe yaron da suka yi garkuwa da shi a Bauchi