Aminiya:
2025-04-13@11:40:11 GMT

Magungunan Jabu: ’Yan majalisa sun nemi yin hukuncin ɗaurin rai da rai

Published: 7th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilan Tarayya ta buƙaci babban lauyan gwamnatin tarayya da ya gabatar da gyare-gyare ga dokokin da ake da su da nufin zartar da hukunci mai tsauri da suka haɗa da ɗaurin rai da rai ga waɗanda ke da hannu wajen sarrafawa da shigo da magungunan jabu.

Da kuma gaggarumin tara ga ’yan kasuwar da aka samu da laifin yin mu’amala da jabun kayayyaki.

’Yan bindiga sun mamaye masallaci da awon gaba da masallata a Sakkwato Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi

Hakan ya biyo bayan wani ƙuduri kan muhimmancinsa ga jama’a da ɗan majalisa, Tolani Shagaya ya gabatar a zauren majalisar a ranar Alhamis.

Ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kafa dokar ta-ɓaci kan barazanar rarrabawa da sayar da magunguna da kayayyakin abinci na jabu, marasa inganci ko waɗanda wa’adin aikin su ya ƙare a ƙasar.

Yayin da yake gabatar da ƙudirin a zauren majalisar, ya ce ƙaruwar sarrafa da shigo da kayayyaki na jabu da marasa inganci da magunguna da abinci da abubuwan sha a faɗin Najeriya na haifar da babbar barazana ga lafiyar al’umma, tsaron ƙasa da kuma tattalin arzikin ƙasa.

Ya ce, “Kwanan nan Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna a Najeriya NAFDAC ta kama jabun kayan abinci da magunguna da suka kai na sama da Naira biliyan 5 a wani samame da suka kai a kasuwar Cemetery Market da ke garin Aba, Jihar Abia lamarin da ya nuna yadda wannan matsalar ke yaduwa.

“Najeriya na fama da asarar tattalin arziki kusan tiriliyan 15 a duk shekara saboda jabun kayayyaki da marasa inganci, kamar yadda Hukumar Daidaita Ma’auni ta Najeriya (SON) ta ruwaito. Yaɗuwar samfuran jabu ba wai kawai yana kawo cikas ga amincin masu amfani ba har ma yana hana saka hannun jari na gaske a masana’antar abinci da magunguna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno

Wani abin takaici ya sake afkuwa a kan hanyar Maiduguri zuwa Damboa a Jihar Borno mai cike da tashin hankali, yayin da wani bam ya tarwatse a safiyar Asabar da rana, inda aƙalla mutane takwas ne suka mutu.

Wasu shaidun gani da ido na nuni da cewa fashewar bam ɗin da ake kyautata zaton mayaƙan Boko ne suka dasa shi ya tarwatsa wata motar bas ƙirar Toyota “Hummer Bus” da ke ɗauke da fasinjoji zuwa Maiduguri babban birnin Jihar Borno.

An kashe Uba da ’ya’yansa biyu a ƙauyen Filato An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano

Wata majiya mai tushe da aka zanta da ita, ta tabbatar da cewa aƙalla mutane bakwai da suka haɗa da direban motar ne ake fargabar sun mutu a wannan mummunan fashewar.

Titin Maiduguri zuwa Damboa ya kasance muhimmiyar hanyar mota da ta haɗa birnin Maiduguri zuwa ƙaramar hukumar Damboa da sauran al’ummomin kudancin Borno wadda a kullum ake fargabar bin ta lura da cewar tana gab da dajin Sambisa.

Don haka wannan lamari na baya-bayan nan ya zama babban abin tunatarwa game da barazanar tsaro da ke fuskantar matafiya da ke bin wannan hanya mai muhimmanci.

Har yanzu dai hukumomin tsaro ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba, har ya zuwa lokacin kammala wannan rahoto.

To sai dai kuma babu shakka wannan harin zai ƙara dagula al’amura game da lafiyar masu tafiye-tafiye da sufuri a yankin da kuma yankin da ake da ’yan tada ƙayar baya a yankin Arewa maso Gabas.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsohon kocin Super Eagles Christian Chukwu ya rasu
  • Fashewar bam a mota ta kashe mutum takwas a Borno
  • An kashe ƙasurgumin ɗan bindiga Gwaska da mayaƙa 100 a Katsina
  • An kama mutum 8 kan faɗan daba a Kano
  • Yadda bom ya tashi da ɗan gwangwan a Legas
  • Najeriya Tana Fatan Samun Dalar Amurka Biliyan $200 A Ayyukan Sararin Samaniya
  • Najeriya Ta Jaddada Aniyar Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing
  • NAJERIYA A YAU: Yadda Faɗuwar Farashin Ɗanyen Mai Zai Shafi Rayuwar ’Yan Najeriya
  • Gwamnatin Kano ta tura tawaga zuwa Edo kan kisan mafarauta
  • E.U.  ta dauki wasu sabbin matakan kalubalantar harajin fito na Amurka