Aminiya:
2025-03-23@22:20:34 GMT

Magungunan Jabu: ’Yan majalisa sun nemi yin hukuncin ɗaurin rai da rai

Published: 7th, February 2025 GMT

Majalisar Wakilan Tarayya ta buƙaci babban lauyan gwamnatin tarayya da ya gabatar da gyare-gyare ga dokokin da ake da su da nufin zartar da hukunci mai tsauri da suka haɗa da ɗaurin rai da rai ga waɗanda ke da hannu wajen sarrafawa da shigo da magungunan jabu.

Da kuma gaggarumin tara ga ’yan kasuwar da aka samu da laifin yin mu’amala da jabun kayayyaki.

’Yan bindiga sun mamaye masallaci da awon gaba da masallata a Sakkwato Lakurawa sun kashe mutum 1 sun jikkata 6 a Kebbi

Hakan ya biyo bayan wani ƙuduri kan muhimmancinsa ga jama’a da ɗan majalisa, Tolani Shagaya ya gabatar a zauren majalisar a ranar Alhamis.

Ta yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kafa dokar ta-ɓaci kan barazanar rarrabawa da sayar da magunguna da kayayyakin abinci na jabu, marasa inganci ko waɗanda wa’adin aikin su ya ƙare a ƙasar.

Yayin da yake gabatar da ƙudirin a zauren majalisar, ya ce ƙaruwar sarrafa da shigo da kayayyaki na jabu da marasa inganci da magunguna da abinci da abubuwan sha a faɗin Najeriya na haifar da babbar barazana ga lafiyar al’umma, tsaron ƙasa da kuma tattalin arzikin ƙasa.

Ya ce, “Kwanan nan Hukumar kula da ingancin abinci da magunguna a Najeriya NAFDAC ta kama jabun kayan abinci da magunguna da suka kai na sama da Naira biliyan 5 a wani samame da suka kai a kasuwar Cemetery Market da ke garin Aba, Jihar Abia lamarin da ya nuna yadda wannan matsalar ke yaduwa.

“Najeriya na fama da asarar tattalin arziki kusan tiriliyan 15 a duk shekara saboda jabun kayayyaki da marasa inganci, kamar yadda Hukumar Daidaita Ma’auni ta Najeriya (SON) ta ruwaito. Yaɗuwar samfuran jabu ba wai kawai yana kawo cikas ga amincin masu amfani ba har ma yana hana saka hannun jari na gaske a masana’antar abinci da magunguna.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Majalisar Wakilai Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa

A cewarsa, domin tabbatar da gudanar da wannan tantancewar, an samar da kwakkwaran kwamitoci a matakin jiha da kananan hukumomi tare da sauran sassan hukumomin da ke da alaka da kudi, sannan an ba su umarni samar da dukkan bayanan biyan albashin nan take.

Farouk ya bukaci ma’aikatan da matsala ta shafa su kai kansu gaban hukumominsu tare da nagartattun bayansu kan dalilin kin bin wannan umarni, saboda a kula da sabunta kundin biyan albashin.

Ya ce Mambobin kwamitin sun hada da manyan sakatarorin daga manyan ma’aikatu, wakilai daga kwamitin tsara jadawalin albashi da kuma wasu manyan jami’an a ofishin sakataren gwamnatin Jihar Kano. Sannan ya jadadda cewa bin wannan umarni ya zama wajibi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Tace Zata Kaddamar Da Sabbin Magunguna Da Ta Samar Tare Da Amfani Da Makamashin Nukliya
  • An Aika Dan Canji Da Dan Walawala Gidan Yari A Kwara
  • Gwamnatin Kano Ga Ma’aikata: Duk Mai Bukatar Aikinsa Dole Ya Gabatar Da Kansa A Wajen Tantancewa
  • Majalisar Wakilai ta musanta karɓar kuɗi kan dokar ta-ɓaci a Ribas
  • Hajjin Bana: Dole A Yi Wa Maniyyatan Bauchi Riga-kafin Foliyo – Hukumar Alhazai
  • Wata Kotu A Abuja Ta Kori Karar Da Karuwai Suka Shigar Gabanta
  • An Bukaci Gwamnati A Kowani Mataki Da Ta Taimakawa Yaki Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Kaduna Ta Raba Abinci, Tufafi Ga Marayu, Mabukata Da Malamai
  • Gwamnatin Yobe na ciyar da almajirai a Tsangayu 85 kullum
  • NAJERIYA A YAU: Illar Sare Itatuwa Ga Sauyin Yanayi Da Lafiyarmu